HausaTv:
2025-07-29@02:37:59 GMT

Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba

Published: 28th, July 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya bayyana cewa Iran a shirye take ta fadada hulda da kasashen turai, amma kuma wannan ba zai sa ta saryar da hakkinta na sarrafa makamashin nukliya karshen dokokin kasa da kasa wadanda suka amince mata ta yi haka ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a yau Litinin a lokacinda yake ganaw da sabon jakadan kasar Faransa a Tehran pierre Cochard wanda ya mika masa tarkardun fara aikinbsa.

Shugaban ya kara da cewa an takurawa kasar Iran dangane da shirinta na makamashin nukliya a bayan. Amma daga yanzun kuma ba zata amince da irin takurawa ta bay aba.

Ya kuma bayyana cewa tattaunawa tsakanin Iran da kasashe uku na turai wato Faransa da Jamus da kuma Burtaniya, saboda samun fahintar juna da kuma daukewa kasar takunkuman tattalin arzikinn da turawan suka dora mata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yawan Mutanen Da Suka Rayukansu A Rikicin Lardin Suwaida Na Kasar Siriya Ya Kai 1,400

Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama ta Siriya ta tattara bayanan mutuwar mutane 1,400 a loardin Sweida na Siriya

Siriya, Faransa da Amurka sun sanar da wata taswirar hadin gwiwa don tabbatar da zaman lafiya a Siriya, bayan tattaunawar da ba a taba ganin irinta ba a birnin Paris na Faransa, wadda ta hada ministan harkokin wajen gwamnatin rikon kwarya na Siriya Asaad al-Sheibani, da takwaransa na Faransa Jean-Noel Barrot da manzon Amurka na musamman a Siriya Tom Barrack.

Sanarwar ta hadin gwiwa da aka fitar bayan taron na bangarorin uku, ta tabbatar da goyon bayan shirin mika mulki ga gwamnatin kasar Siriya da karfafa hadin kan al’umma, musamman a birnin Sweida da ke arewa maso gabashin kasar Siriya, da hadin gwiwa wajen yaki da ta’addanci, da tabbatar da cewa babu wata jam’iyya da za ta kawo barazana ga zaman lafiyar yankin.

Wakilin Amurka na musamman a Siriya Tom Barak ya bayyana tattaunawar ta Paris a matsayin wani abin koyi na diflomasiyya mai tsauri da ke kawo karshen rikice-rikice, yana mai jaddada cewa kasarsa za ta ci gaba da hada kai da kawayenta wajen gina Siriya mai tsaro da hadin kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a Darazo
  • VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kiran Cewa; Ina Masu Fafatukar Kare Hakkin Dan Adam Suke A Bala’in Gaza?
  • DR Congo: M23 Ta Yi Barazanar Kauracewa Sulhu da Gwamnatin Kongo
  • Jagora: Za’a Gaggauta Ci Gaba A Ilmi Da Fasahar Tsaron Sojojin Kasar
  • Rasha Ta Sha Alwashin Mayar Wa Da Nato Martani Mai Tsanani Idan Ta Kai Ma Ta Hari
  • Faransa Ta Saki Dan GWagwarmayar Kasar Lebanon Goerge Abdullah Ya Bayan Zaman Kurkuku Na Shekaru 41
  • Yawan Mutanen Da Suka Rayukansu A Rikicin Lardin Suwaida Na Kasar Siriya Ya Kai 1,400
  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Nuna Sha’awar Ganawa Da Shugaban Kasar Rasha