Aminiya:
2025-07-28@20:52:18 GMT

Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano

Published: 28th, July 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta sanar da cewa akwai aƙalla fiye da mutum miliyan 1.2 da ke fama da ciwon hanta da ake kira Hepatitis B a faɗin jihar.

Kwamishinan Lafiya, Dokta Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yau Litinin yayin wani taron manema labarai a Cibiyar Tiyata ta Gaggawa da ke Asibitin Nasarawa a birnin Dabo.

Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000 An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja

Aminiya ta ruwaito cewa wannan sanarwar na zuwa ne a daidai Ranar Ciwon Hanta ta Duniya ta bana.

Kwamishinan ya bayyana ciwon hanta a matsayin matsala babba da ana iya magance ta matuƙar an miƙe tsaye a kai.

Ya yi bayanin cewa muddin ba a farga ba ko kuma aka yi sakaci, cutar tana iya shafar ƙoda ko ma ta rikiɗe zuwa ciwon daji.

Dokta Labaran ya sanar da cewa Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan domin tallafa wa ƙoƙarin da take yi na aiwatar da shirin daƙile yaɗuwar ciwon hantar a tsakanin mata da jaririnsu da ake kira “HepFree UwadaJariri”— wanda aka ƙaddamar tun a watan Fabrairun bana.

Kano ita ce jihar ta farko a Nijeriya da ta ƙaddamar tare da ware kuɗi domin shirin nan na daƙile ciwon hanta ta hanyar duba lafiya da kuma bai wa mata masu juna biyu magani kyauta waɗanda aka gano suna ɗauke da cutar.

Kwamishinan ya ce ana gudanar da wannan aiki a manyan cibiyoyin lafiya bakwai da suka haɗa da Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, da Asibiti Ƙwararru na Murtala Muhammad, da Asibitin Koyarwa na Abdullahi Wase, da manyan Asibitoci da ke garin Bichi, da Gaya, da kuma Wudil.

Yau ce ranar yaƙi da cutar ciwon hanta ta duniya wadda ta yi daidai da 28 ga watan Yuli.

Hukumar Lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce mutane da dama ne ke ɗauke da wannan cuta wadda a Turance ake kira Hepatitis, amma ba tare da sun sani ba.

Alƙaluma sun nuna cewa, miliyoyin mutane ne cutar ta Hepatitis ke hallakawa a faɗin duniya.

An dai ware wannan rana ne domin jawo hankali ga illar wannan cutar, da kuma hanyoyin da ya kamata a bi domin shawo kanta.

Likitoci na shawartar al’umma da su riƙa zuwa gwajin cutar domin ba kasafai take nuna alamu ba kafin ta yi tsanani.

Shi dai ciwon hanta ko kuma Hepatitis na da nau’i kashi biyar da suka haɗa da:

Ciwon hanta ajin A
Ciwon hanta ajin B
Ciwon hanta ajin C
Ciwon hanta ajin D
Ciwon hanta ajin E

Sai dai ƙwararru sun ce nau’in da suka fi illa da haɗari su ne ajin A da na B wata Hepatitis A da Hepatitis B.

Shi ciwon hanta ajin B wato Hepatitis B yana da rigakafi. Amma Hepatitis C ba shi da rigakafi amma kuma maganinta na warkarwa ɗari bisa ɗari, a cewar ƙwararru.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An gano gwawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja

An gano gwawar mutum 15 a yayin da ake ci gaba neman wasu uku bayan hastarin kwalekwale da ya auku a yankin Ƙaramar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja.

Kwalekwalen ya kife ne a yayin da yake ɗauke da mutum 43 da buhuna 60 na shansherar shinkafa da shanu uku da tumaki biyu a ranar Asabar.

Kifewar kwalekwalen ta auku ne a sakamakon karonsa da wani kututture bayan ya ɗauki fasinjojin daga yankin Guni zai kai su kasuwar mako-mako da ke yankin Zumba da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro.

Manajan Hukumar Albarkatun Koguna ta Ƙasa (NIWA), mai kula da yankin, Akapo Adeboye, ya ce an gano gwawar mutum 15, amma ana ci gaba neman wasu mutum uku, ko da yake cewa an yi nasarar ceto mutum 26 da ke sanye da rigunan kariya da ransu, bayan aukuwar hatsarin.

HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INEC

Adebayo ya bayyana cewa, “Mutanen sun taso ne daga ƙauyen Shayita za su tafi Kasuwar Kwata da ke Zumba tare da kayansu na miliyoyin kuɗaɗe a ranar Asabar 26 ga watan Yuli, 2025.

“Jami’an NIWA sun gudanar da aikin ceto, amma an samu asarar rayuka 18, an ceto wasu 26, kuma aka ci gaba da aiki da kuma ƙoƙarin kamo mai kwalekwalen.”

Shaidu sun ce hastarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na ranar Asabar, kuma yawancin fasinjojin mata ne da ƙananan yara, kuma jami’an Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) sun tabbatar da hakan.

Sarkin Ruwan Zumba, Umar Isah, ya ce mutum 15 ne suka rasu, an ceto 25, amma an yi asarar shanu uku da buhu 60 na shansherar shinkafa.

“A cikin mutum 15 da suka rasu har da ƙananan yara uku mata da gano gawarwakinsu,” in ji shi.

Amma Darakta Janar na Hukumar NSEMA, Abdullahi Baba Arah, ya ce gawa 13 aka gano kuma an yi jana’izarsu a ranar Lahadi.

Arah, wanda ya tabbatar da asarar wasu mutane da dabbobi da kayan abinci a hatsarin, ya ce gawarwakin sun haɗa da mata takwas da maza uku da kuma yara biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
  • An gano gwawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
  • Taron ‘Kasashe biyu’ A Gefen Taron MDD A NewYork
  • Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a Darazo
  • Dole gyaran kundin tsarin mulki ya haɗa kan ƙasa da shugabanci na gari — Abba
  • Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159
  • Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50