Aminiya:
2025-09-17@23:26:17 GMT

Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano

Published: 28th, July 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta sanar da cewa akwai aƙalla fiye da mutum miliyan 1.2 da ke fama da ciwon hanta da ake kira Hepatitis B a faɗin jihar.

Kwamishinan Lafiya, Dokta Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yau Litinin yayin wani taron manema labarai a Cibiyar Tiyata ta Gaggawa da ke Asibitin Nasarawa a birnin Dabo.

Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000 An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja

Aminiya ta ruwaito cewa wannan sanarwar na zuwa ne a daidai Ranar Ciwon Hanta ta Duniya ta bana.

Kwamishinan ya bayyana ciwon hanta a matsayin matsala babba da ana iya magance ta matuƙar an miƙe tsaye a kai.

Ya yi bayanin cewa muddin ba a farga ba ko kuma aka yi sakaci, cutar tana iya shafar ƙoda ko ma ta rikiɗe zuwa ciwon daji.

Dokta Labaran ya sanar da cewa Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan domin tallafa wa ƙoƙarin da take yi na aiwatar da shirin daƙile yaɗuwar ciwon hantar a tsakanin mata da jaririnsu da ake kira “HepFree UwadaJariri”— wanda aka ƙaddamar tun a watan Fabrairun bana.

Kano ita ce jihar ta farko a Nijeriya da ta ƙaddamar tare da ware kuɗi domin shirin nan na daƙile ciwon hanta ta hanyar duba lafiya da kuma bai wa mata masu juna biyu magani kyauta waɗanda aka gano suna ɗauke da cutar.

Kwamishinan ya ce ana gudanar da wannan aiki a manyan cibiyoyin lafiya bakwai da suka haɗa da Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, da Asibiti Ƙwararru na Murtala Muhammad, da Asibitin Koyarwa na Abdullahi Wase, da manyan Asibitoci da ke garin Bichi, da Gaya, da kuma Wudil.

Yau ce ranar yaƙi da cutar ciwon hanta ta duniya wadda ta yi daidai da 28 ga watan Yuli.

Hukumar Lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce mutane da dama ne ke ɗauke da wannan cuta wadda a Turance ake kira Hepatitis, amma ba tare da sun sani ba.

Alƙaluma sun nuna cewa, miliyoyin mutane ne cutar ta Hepatitis ke hallakawa a faɗin duniya.

An dai ware wannan rana ne domin jawo hankali ga illar wannan cutar, da kuma hanyoyin da ya kamata a bi domin shawo kanta.

Likitoci na shawartar al’umma da su riƙa zuwa gwajin cutar domin ba kasafai take nuna alamu ba kafin ta yi tsanani.

Shi dai ciwon hanta ko kuma Hepatitis na da nau’i kashi biyar da suka haɗa da:

Ciwon hanta ajin A
Ciwon hanta ajin B
Ciwon hanta ajin C
Ciwon hanta ajin D
Ciwon hanta ajin E

Sai dai ƙwararru sun ce nau’in da suka fi illa da haɗari su ne ajin A da na B wata Hepatitis A da Hepatitis B.

Shi ciwon hanta ajin B wato Hepatitis B yana da rigakafi. Amma Hepatitis C ba shi da rigakafi amma kuma maganinta na warkarwa ɗari bisa ɗari, a cewar ƙwararru.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027.

Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta.

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo

“Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna cewa ba sa son a samu hamayya a lokacin zaɓe,” in ji shi.

Galadima ya kuma yi gargadi kan shirin nada wani da ya kira mai lam’a a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin rudani.

“Ina fatan ba gaskiya ba ne, domin idan wannan mutumin ya zama shugaban INEC, ka tabbata cewa wannan gwamnati na neman tayar da yaƙin basasa,” in ji shi.

Sai dai bai ambaci sunan mutumin ba.

Dangane da batun fara yaƙin neman zaɓe da wuri da wasu jam’iyyu ke yi, Buba Galadima ya zargi INEC da gazawa wajen aiwatar da tanade-tanaden dokokin zaɓe.

“Wannan batun fara yaƙin neman zaɓe kafin INEC ta ba da izini, gwamnatin da ke kan mulki ce ta fara shi. Wannan yana nuna cewa INEC ba za ta iya zama mai adalci a irin wannan yanayin siyasa da muke ciki ba,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa