Matashi ya daɓa wa abokinsa wuƙa a kan budurwa
Published: 3rd, April 2025 GMT
Wani matashi mai shekaru 27, Rabiu Suleiman, ya daɓa wa abokinsa Yunusa Muazu wuƙa, tare da yi masa mummunan rauni, a kan budurwa a yankin Gwagwalada da ke Abuja.
Lamarin ya faru ne a daren Talata a wani gidan kallon fina-finai a Unguwar Dodo.
NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ‘Ya’yansu Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Galadiman Kano, Abbas SanusiSuleiman ya zargi Muazu da yin soyayya da budurwarsa wadda yake shirin Jamila Yakubu.
Faɗan ya fara ne lokacin da Suleiman ya samu Jamila da Muazu suna tattaunawa a gidan kallon fina-finan.
Suleiman, ya fusata lokacin da ya ga Jamila tare da abokinsa, sai ya tafi kai-tsaye ya hau abokinsa da duka.
A lokacin da suke faɗa , Suleiman ya fito da wuƙa sannan ya daɓa wa Muazu a gadon baya.
Wannan abu ya ja hankalin wasu daga cikin mutanen da ke cikin gidan kallon, wanda hakan ya sa aka yi gaggawar kiran ’yan sanda, kuma nan take suka tafi da Suleiman.
An kai Muazu zuwa asibiti domin kula da shi.
Kakakin rundunar ’yan sandan birnin tarayya, SP Josephine Adeh, ba ta amsa kira da saƙonnin waya kan lamarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faɗa Gwagwalada zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
Ministan kiwon lafiya na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Muhammad Ridha Zafarqandi ya tattauna hanyoyin bunkasa aiki tare a fagen kiwon lafiya da mataimakin ministan kiwon lafiya na tarayyar kasar Rasha.
Ministan na Iran dai ya yi wannan trattaunar ne a jiya Lahadi inda su ka tabo fagage da dama da su ka yi tarayya akansu a cikin harkar kiwon lafiya.
Ministan na Iran ya kuma ce, a baya kasashen biyu sun cimma yarjejeniya wacce a wannan lokacin ake son bunkasa ta.
Muhammmad Ridha Ya kuma bayyana yadda kasashen biyu suke da kayan aiki masu yawa a fagagen magance cutuka masu yaduwa da wdanda ba su yaduwa haka nan kuma fagen yin magunguna.
Shi kuwa mataimakin ministan kiwon lafiyar na tarayyar Rasha Olog Silgy ya tabbatar da cewa,kasarsa a shirye take ta bunkasa aiki da jamhuriyar musulunci ta Iran a fagen musayar dalibai da kuma nazarce-nazarce da bincike na ilimin likitanci.
Kasashen biyu sun kafa kwamitin hadin gwiwa na yin fada da cutuka masu yaduwa da zai taka rawa mai girma wajen magance cutuka.