Matashi ya daɓa wa abokinsa wuƙa a kan budurwa
Published: 3rd, April 2025 GMT
Wani matashi mai shekaru 27, Rabiu Suleiman, ya daɓa wa abokinsa Yunusa Muazu wuƙa, tare da yi masa mummunan rauni, a kan budurwa a yankin Gwagwalada da ke Abuja.
Lamarin ya faru ne a daren Talata a wani gidan kallon fina-finai a Unguwar Dodo.
NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ‘Ya’yansu Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Galadiman Kano, Abbas SanusiSuleiman ya zargi Muazu da yin soyayya da budurwarsa wadda yake shirin Jamila Yakubu.
Faɗan ya fara ne lokacin da Suleiman ya samu Jamila da Muazu suna tattaunawa a gidan kallon fina-finan.
Suleiman, ya fusata lokacin da ya ga Jamila tare da abokinsa, sai ya tafi kai-tsaye ya hau abokinsa da duka.
A lokacin da suke faɗa , Suleiman ya fito da wuƙa sannan ya daɓa wa Muazu a gadon baya.
Wannan abu ya ja hankalin wasu daga cikin mutanen da ke cikin gidan kallon, wanda hakan ya sa aka yi gaggawar kiran ’yan sanda, kuma nan take suka tafi da Suleiman.
An kai Muazu zuwa asibiti domin kula da shi.
Kakakin rundunar ’yan sandan birnin tarayya, SP Josephine Adeh, ba ta amsa kira da saƙonnin waya kan lamarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faɗa Gwagwalada zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da aniyar ta ta bunƙasa harkar kiwon dabbobi a Nijeriya a matsayin wata muhimmiyar hanya ta magance rikice-rikicen da ke tsakanin manoma da makiyaya, tare da amfani da damar tattalin arzikin da ke cikin ɓangaren.
Ɗaya daga cikin Shugabannin Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Harkar Kiwo, Farfesa Attahiru Jega, shi ne ya bayyana hakan a wurin taron tattaunawa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa, wanda Gidauniyar Sa Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna, a ranar Laraba.
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyarJega ya bayyana cewa sabuwar Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo tana ɗaya daga cikin ginshiƙan da ke cikin shirin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na sauya fasalin ɓangaren kiwon dabbobi.
Ya jaddada cewa ana aiwatar da hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba tare da son rai na siyasa ba, tare da mayar da hankali kan haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, al’ummomin makiyaya da sauran muhimman masu ruwa da tsaki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp