Aminiya:
2025-11-02@19:45:29 GMT

Janar Tsiga ya kuɓuta bayan shafe kwana 56 a hannun ’yan bindiga

Published: 3rd, April 2025 GMT

Birgediya-Janar Maharazu Tsiga (mai ritaya), ya kuɓuta bayan shafe kwana 56 a hannun ’yan bindiga.

An sace Janar Tsiga, wanda Tsohon Shugaban Hukumar NYSC ne, a garinsu da ke Ƙaramar Hukumar Bakori a Jihar Katsina, a ranar 5 ga watan Fabrairu, 2025.

Mutum ɗaya ya rasu, 3 sun jikkata a rikicin ’yan sara-suka a Filato HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman Kano

Hakazalika, aharan sun sace mutum tara a tare da shi a lokacin da suka kai harin.

Duk da cewa iyalansa sun biya kuɗin fansa, ’yan bindigar sun ci gaba da tsare shi na tsawon makonni.

Rahotanni sun nuna cewa har yanzu ba a san adadin kuɗin da aka biya a matsayin kuɗin fansar ba.

Wasu sun ce Naira miliyan 60 aka biya, amma wasu majiyoyi masu tushe sun ce an biya sama da haka.

Wani daga cikin iyalansa ya bayyana cewa bayan maharan sun karɓi kuɗin, sai suka yi shiru har na tsawon mako guda, kafin daga bisani su kira iyalansa a ranar 11 ga watan Maris, inda suka ba shi ya yi magana da su.

Daga baya, sun sake neman ƙarin kuɗi, amma iyalan nasa ba su ƙara musu ba.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa yanzu haka yana Jihar Zamfara, wanda daga nan za a kai shi Abuja.

Wani jami’in soja ya tabbatar da sakinsa, inda ya ce yana cikin ƙoshin lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari Janar Tsiga

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 

Majalisar Shugabannin Kudancin Kaduna (SKLC) ta kammala shirye-shirye domin gudanar da gagarumar tarbar ga tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya).

Za a yi bikin ne domin tunawa da kyakkyawar rawar da majalisar ta ce ya taka a aikin soja da kuma hidimarsa ga kasa.

An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure

An shirya gudanar da bikin ne a ranar Asabar, 22 ga watan Nuwamba, 2025, a Babban Filin Wasan na garin Kafanchan, cibiyar kasuwancin Kudancin Kaduna.

A yayin taron majalisar karo na 19 da aka gudanar a Kafanchan, Shugaban SKLC, Ishaya Dare Akau, ya ce za a ba Janar Musa lambar yabo mafi girma ta majalisar wato GCSK.

Akau, ya ce wannan karramawar tana nuni da yadda Janar Musa ya wakilci Kudancin Kaduna, Jihar Kaduna, da Najeriya baki daya cikin kwarewa da cancanta, inda ya bayyana shi a matsayin jakada nagari.

A yayin taron, majalisar ta kuma kaddamar da kwamitin kula da harkokin kudi na Bikin Gargajiya na Shekara-shekara na Kudancin Kaduna (SKFEST), inda aka nada Shugaban Hukumar Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS), Comrade Jerry Adams, a matsayin shugaban kwamitin.

Manyan jami’an gwamnati da dama sun halarci taron karkashin jagorancin Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Henry Danjuma Magaji, tare da Mai ba Gwamna shawara kan harkokin siyasa, Hon. Ado Dogo Audu.

Sun yi wa majalisar bayani kan muhimman shirye-shiryen gwamnati, ciki har da amincewar da gwamnatin tarayya ta bayar na farfado da aikin gina hanyar Jere–Kagarko–Jaba–Kwoi–Kafanchan, wadda Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya taimaka wajen ganin tabbatuwarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku