Aminiya:
2025-07-11@09:35:50 GMT

An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas

Published: 30th, April 2025 GMT

Wata tsohuwa mai shekara 80 a kasar Turkiyya za ta shafe sama da shekara 4 a gidan yari, saboda ta daki jikarta ’yar shekara 18 da silifa a lokacin da suke takaddama.

Asiye Kaytan na zaune tare da jikarta Vural a unguwar Topraklık da ke Denizli a Kudu maso Yammacin Turkiyya.

Tuntuni dai iyayen yarinyar suka rabu, inda tsohuwar mai shekara 80 take kulawa da ita fiye da kanta.

A ranar 9 ga Agustan bara, bayan Vural ta dawo daga aiki, ta fada wa kakarta cewa, za ta fita waje tare da wasu abokanta.

Tsohuwar ta ji tsoron fitar don kare lafiyarta, ta ce ba za ta yarda ba, har ma ta kulle kofa don tabbatar da cewa Vural ba ta iya fita ba.

Zuwa wani lokaci, sai budurwar ta yi kokarin bude kofar, inda Kaytan ta dauko takalmi silifas, ta dake ta.

Vural ta rama dukan da kakarta ta yi mata a ka da wayarta. Kaytan ta fara zubar da jini, inda yarinyar ta kira motar asibiti.

“Jikata ta so fita da yamma, amma na hana ta, na kulle kofa,”

Kaytan ta shaida wa jaridar Sabah News. “Na buge ta a hannu da silifas, sai ta buge ni da wayarta a ka. Lokacin da na fara zubar da jini, sai ta tsorata ta kira motar daukar marasa lafiya.”

Kaytan da jikarta ba su kai kara a kan junansu ba, amma sun bayyana wa wadanda suka amsa da farko yadda tsohuwar ta samu rauni a ka, inda suka kai rahoto a asibitin Jihar Denizli, wanda daga baya aka mika wa ’yan sandan yankin.

An gayyaci matan biyu domin amsa tambayoyi, kuma duk da bayyana cewa sun sasanta rikicin nasu kuma sun yi sulhu, sai aka buɗe ƙofar ƙarar jama’a, kuma ofishin mai shigar da kara na gwamnati ya shigar da karar kakar mai shekara 80.

A shari’ar tasu, masu gabatar da kara sun yi zargin cewa, silifas da Kaytan ta yi amfani da shi wajen dukan jikarta makami ne, kuma yarinyar ’yar shekara 18 ta yi kokarin kare kanta ne a lokacin da ta bugi kakarta da wayarta.

An kuma tuhumi kakar da tauye ’yancin dan-adam saboda ta kulle Vural a cikin gidanta tare da hana ta fita, zargin da zai iya kai ga hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari.

A ranar 25 ga watan Fabrairu ne kotun hukunta manyan laifuka ta 12 ta kasar ta yanke wa Asiye Kaytan hukuncin daurin shekaru 2 da wata 6 a gidan yari saboda laifin ‘tauye ’yancin dan-adam ta hanyar amfani da karfi ko barazana ko yaudara da kuma ƙarin shekaru 2 da watanni 6 kan amfani da “makami” wajen aikata laifin da ta yi wa jikarta.

Daga ƙarshe an rage hukuncin zuwa shekaru 4 da watanni 2, amma lauyan Kaytan ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin.

Idan kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke mata, za ta je gidan yari.

“Zan shiga kurkuku ina da shekara 80? Ta yaya zan zauna a can? An yi mini tiyata, kuma ina tafiya da kyar, za su saka ni a kurkuku saboda silifas,” tsohuwar ta yi kuka.

‘‘Babu wanda ya isa ya daki yaronsa da silifas saboda ana daukar sa a matsayin makami. Ba ni da masaniyan cewa silifas ya zama makami’’, in ji ta. “

An yi wa kakata hukuncin zaman gidan yari ne saboda ta doke ni da silifas, ta hana ni fita daga gidan. Ban so haka ta kasance ba, ban kai karar ta ba, amma an bude karar jama’a,” in ji Asiye Vural.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tsohuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha, ya ce ba Shugaban Kasa Bola Tinubu kaɗi ne ya sa Muhammadu Buhari ya ci zabensa a shekarar 2015 ba.

Ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi a Abuja ranar Laraba, yayin kaddamar da littafin da mai magana da yawun tsohon Shugaba Buhari, Malam Garba Shehu ya wallafa kan abubuwan da ya gani a zamanin mulkinsu.

Buhari dai ya shugabanci Najeriya ne daga shekarar 2015 zuwa 2023.

’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II

Daga cikin manyan bakin da suka halarci kaddamar da littafin akwai tsohon Shugaban Kasa na mulkin soja, Yakubu Gowon da tsohon Mataimakan Shugaban Kasa, Atiku Abubakar da Yemi Osinbajo da Sakataren Gwamnatin Tarayya mai ci, George Akume da dai sauransu.

Idan za a iya tunawa, yayin wani taron neman goyon bayan wakilan jam’iyyar APC a jihar Ogun a aranar daya ga watan Yunin 2022 gabanin zaben fi-da-gwani na jam’iyyar, Tinubu ya yi ikirarin cewa da ba dan shi ba, da Buhari bai ci zaben 2015 ba.

To sai dai da yake gabatar da mukala a kan nasarorin mulkin Buhari, Boss ya ce akwai jiga-jigan APC da dama da suka taimaka aka sami nasarar, ba wai Tinubu shi kadai ba, yana mai cewa gaskiya da rikon amanar Buharin ma sun taka rawa.

Ya ce, “Akwai kuma bangarorin jam’iyyar CPC ita kanta, akwai na ANPP da na ACN da APGA da kuma wani tsagi na PDP da ya balle ya shigo cikin hadakar APC. Tinubu ya taka rawar gani, sannan Sanata Ali Modu Sheriff wanda tsohon Shugaban Kwamitin Amintattu ne na ANPP shi ma ya yi kokari.

“Hadakar ta yi nasarar kafa tarihin farko a Najeriya inda aka kayar da shugaba mai ci, kuma gaskiya da rikon amanar shi su ne a kan gaba wajen samun wannan nasarar.

“A bangarenmu na ACN, ba na so na tayar da kura, amma makasudin hada majar ita ce don a tsayar da Buhari takara saboda mun kalli alkaluman kuri’unsa na baya.

“A shekara ta 2003, an fafata tsakanin Buhari da Obasanjo, inda Buharin ya sami kuri’a miliyan 2.7. A 2007 kuma, ya sami miliyan 6.6, sai a 2011 kuma ta karu zuwa 12.2.

“Lokacin da muka kokarin hada APC, jam’iyyar CPC ta Buhari na da Gwamna daya, ACN na da shida, sai ANPP na da uku. Idan ka hada jimlar kuri’un da muka samu a zaben Shugaban Kasa a 2015 kuma miliyan 15.4 ne.

“Ka ga ke nan kuri’un da muka kara wa Buhari bayan kafa APC a kan kuri’u miliyan 12.5 din da Buhari ya zo da su daga CPC su ne miliyan uku,” in ji Boss Mustapha.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
  • Kotun ƙoli ta tabbatar da Okpebholo a matsayin gwamnan Edo
  • Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
  • Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha
  • Yemen Ta Nutsarda Wani Jirgin Ruwana HKI Saboda Sabawa Haramcin Wucewa Ta Red Sea
  • HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025
  • Gamayyar ‘Yan Adawa Sun Kaddamar ADC A Gombe  
  • Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ta Godewa JMI Dangane Da Tallafawa Kungiyar Saboda Gwagwarmaya Da HKI
  • Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda
  • An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya