Aminiya:
2025-05-18@15:41:31 GMT

An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas

Published: 30th, April 2025 GMT

Wata tsohuwa mai shekara 80 a kasar Turkiyya za ta shafe sama da shekara 4 a gidan yari, saboda ta daki jikarta ’yar shekara 18 da silifa a lokacin da suke takaddama.

Asiye Kaytan na zaune tare da jikarta Vural a unguwar Topraklık da ke Denizli a Kudu maso Yammacin Turkiyya.

Tuntuni dai iyayen yarinyar suka rabu, inda tsohuwar mai shekara 80 take kulawa da ita fiye da kanta.

A ranar 9 ga Agustan bara, bayan Vural ta dawo daga aiki, ta fada wa kakarta cewa, za ta fita waje tare da wasu abokanta.

Tsohuwar ta ji tsoron fitar don kare lafiyarta, ta ce ba za ta yarda ba, har ma ta kulle kofa don tabbatar da cewa Vural ba ta iya fita ba.

Zuwa wani lokaci, sai budurwar ta yi kokarin bude kofar, inda Kaytan ta dauko takalmi silifas, ta dake ta.

Vural ta rama dukan da kakarta ta yi mata a ka da wayarta. Kaytan ta fara zubar da jini, inda yarinyar ta kira motar asibiti.

“Jikata ta so fita da yamma, amma na hana ta, na kulle kofa,”

Kaytan ta shaida wa jaridar Sabah News. “Na buge ta a hannu da silifas, sai ta buge ni da wayarta a ka. Lokacin da na fara zubar da jini, sai ta tsorata ta kira motar daukar marasa lafiya.”

Kaytan da jikarta ba su kai kara a kan junansu ba, amma sun bayyana wa wadanda suka amsa da farko yadda tsohuwar ta samu rauni a ka, inda suka kai rahoto a asibitin Jihar Denizli, wanda daga baya aka mika wa ’yan sandan yankin.

An gayyaci matan biyu domin amsa tambayoyi, kuma duk da bayyana cewa sun sasanta rikicin nasu kuma sun yi sulhu, sai aka buɗe ƙofar ƙarar jama’a, kuma ofishin mai shigar da kara na gwamnati ya shigar da karar kakar mai shekara 80.

A shari’ar tasu, masu gabatar da kara sun yi zargin cewa, silifas da Kaytan ta yi amfani da shi wajen dukan jikarta makami ne, kuma yarinyar ’yar shekara 18 ta yi kokarin kare kanta ne a lokacin da ta bugi kakarta da wayarta.

An kuma tuhumi kakar da tauye ’yancin dan-adam saboda ta kulle Vural a cikin gidanta tare da hana ta fita, zargin da zai iya kai ga hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari.

A ranar 25 ga watan Fabrairu ne kotun hukunta manyan laifuka ta 12 ta kasar ta yanke wa Asiye Kaytan hukuncin daurin shekaru 2 da wata 6 a gidan yari saboda laifin ‘tauye ’yancin dan-adam ta hanyar amfani da karfi ko barazana ko yaudara da kuma ƙarin shekaru 2 da watanni 6 kan amfani da “makami” wajen aikata laifin da ta yi wa jikarta.

Daga ƙarshe an rage hukuncin zuwa shekaru 4 da watanni 2, amma lauyan Kaytan ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin.

Idan kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke mata, za ta je gidan yari.

“Zan shiga kurkuku ina da shekara 80? Ta yaya zan zauna a can? An yi mini tiyata, kuma ina tafiya da kyar, za su saka ni a kurkuku saboda silifas,” tsohuwar ta yi kuka.

‘‘Babu wanda ya isa ya daki yaronsa da silifas saboda ana daukar sa a matsayin makami. Ba ni da masaniyan cewa silifas ya zama makami’’, in ji ta. “

An yi wa kakata hukuncin zaman gidan yari ne saboda ta doke ni da silifas, ta hana ni fita daga gidan. Ban so haka ta kasance ba, ban kai karar ta ba, amma an bude karar jama’a,” in ji Asiye Vural.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tsohuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Senegal ta karbi wani sansaninta na uku daga hannun Faransa

Kasar Faransa ta mika iko na sansanin soja na Contre-Amiral Protet ga kasar Senegel, wanda shi ne sansanin soja na 3 da aka mikawa kasar a bana.

An mika sauran sansanoni biyu da suka hada da Marechal da Sanit-Exupery ne a watan Maris din da ya gabata, Kuma dukkan sansanonin na da mazauni ne a Dakar, babban birnin Senegal.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin Faransa ya fitar, ta ce an tsara mika dukkan wasu sansanonin dake karkarshin ikon Faransa a Senegal a bana, biyo bayan yarjejeniyar da kasashen biyu suka yi.

A ranar 31 ga watan Disamban 2024, shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye ya sanar a jawabinsa na sabuwar shekara cewa, za a bukaci dakarun Faransa su fara janyewa daga kasar a bana.

A shekarun baya bayan nan dai kasashen Afrika sun yi ta kira da janye dakarun Faransa daga kasashensu.

Shi ma a jawabinsa na sabuwar shekara, shugaban Ivory Coast Alassane Ouattara, ya gabatar da shirin ficewar dakarun Faransa daga kasarsa.

Tun tuni daga kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar suka raba gari da kasar ta Faransa tare da yanke alakar soji a tsakaninsu, sai kuma kasar Chadi wacce ta bi sahu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan Kwankwaso
  • Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh                                                                                                              
  • Sojojin Libiya Sun ‘Yantar Da Fursunoni Daga Gidajen Yarin Sirri Da Ake Tsare Da Su Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Senegal ta karbi wani sansaninta na uku daga hannun Faransa
  • Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar
  • Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • An kama wasu da haramtaccen buhunan takin zamani 20 a Borno
  • Kotu ta ɗaure matashi kan wulaƙanta Naira a TikTok