Aminiya:
2025-07-10@13:25:12 GMT

Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina

Published: 21st, March 2025 GMT

Dakarun Sojin Najeriya sun kuɓutar da mutum 84 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Kankara a Jihar Katsina.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Nasir Mu’azu, ya bayyana cewa sojojin runduna ta 17 tare da tallafin jiragen yaƙi sun kai farmaki maɓoyar ’yan ta’adda da ke yankin Sanusi Dutsin-Ma da tsaunukan Pauwa.

’Yan bindiga sun sace shugaban kasuwar kayan miya ta Akinyele a Oyo Farashin fetur na iya tashi bayan Dangote ya daina sayar da mai a Naira

Ya ce a yayin farmakin dakarun sun kashe wasu daga cikin ’yan bindiga sannan suka kuɓutar da waɗanda aka sace.

Daga cikin mutanen da aka ceto, akwai maza bakwai, mata 23, da yara 54.

Kwamishinan ya ce gwamnatin jihar ta yaba wa sojojin bisa ƙoƙarinsu, kuma tuni aka samar da abinci da kulawa ga mutanen da aka kuɓutar, kafin a mayar da su ga iyalansu.

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Katsina ba za ta yi sulhu da ’yan ta’adda ba, domin tana da niyyar ci gaba da yaƙi da su har sai an daƙile matsalar garkuwa da mutane a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakaru Garkuwa Kwamishina yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Har Yanzu Ba A Ga Mutum 160 Bayan Ambaliyar Texas

Gwamnan jihar Texas ta Amurka ya ce sama da mutane 160 ne har yanzu ba a gano ba sakamakon ambaliyar ruwa da ta auku a ranar Juma’ar da ta gabata.

Greg Abbott ya ce wannan adadi na lardin Kerr ne kaɗai, ɗaya daga cikin wuraren da lamarin ya fi muni.

Hukumomi dai sun bayar da rahoton mutuwar fiye da mutum 100.

Masu aikin ceto na aiki a sannu a ƙoƙarin kawar da tarkacen da ruwan ya janyo domin gano ko akwai mutanen da ke maƙale a ƙarƙashinsu musamman a yankin gaɓar kogin Guadalupe.

A jihar New Mexico da ke makwabtaka da Texas, ruwa ya tafi da wani gida inda wani uba ke zaune da ‘ya’yansa biyu a yankin Ruidoso, kuma har anzu ana kan nemansu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja
  • Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina
  • Har Yanzu Ba A Ga Mutum 160 Bayan Ambaliyar Texas
  • Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda
  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato
  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Yobe
  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Gombe