Lamido ya kasance tsohon sakataren jam’iyyar SDP, ya sake jaddada alkawarinsa ga PDP, yana mai cewa bai ga dalilin barinsa jam’iyyar ba.

Lokacin da na kasance sakataren jam’iyyar SDP, ina El-Rufai yake? Ina Shehu Gabam, shugaban jam’iyyar na kasa na yanzu? Duk da kalubalen da PDP ke fuskanta, a nan ne aka haife shi a siyasa.

Idan yana ikirarin cewa PDP ta mutu, to ya manta da asalinsa.”
Yana jaddada cewa El-Rufa’i ya samu nasara ne a siyasa ciki har da mukamin minista da ya rike sakamakon jam’iyyar PDP ne. A cewarsa, duk abin da ya mallaka a yanzu, ya samu ne ta sanadiyyar jam’iyyar PDP ne.

Lamido ya ce ya samu damar barin PDP ciki har da lokacin da jam’iyya suka yi hadaka wajen haifar APC a 2014, amma ya zabi ya ci gaba da zama a PDP. Ya ce wadanda suka bar jam’iyyar a baya sun yi haka ne saboda fushi, inda suka dunga aibata PDP, to amma yanzu me jam’iyyar APC ta yi musu?

Haka kuma, Lamido ya nanata cewa bai kamata a nemi shugabanci wajen bacin rai na kashin kai ba, shugabanci yana bukatar hakuri, juriya, yi wa al’umma hidima da kuma kasa gaba daya. Ya ce neman shugabanci ta hanyar fusata yana kasancewa ne ta kashin kai ba ta al’ummar kasa ba.

Ya yi gargadin cewa ka da a yi adawa da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ta hanyar bukata ta kashin kai ko yin ramako. Ya ce idan manufar ita ce kawar da Tinubu kan karagar mulki, fushi ba shi ne hanya ba. Ya ce ya san yadda zai fuskanci adawa ta fusata.

Lamido ya yi kira a samar da shugabanci mai cike da adalci da kuma martaba hakkokin al’umma. Ya ce ya kamata a mayar da hankali wajen samar da shugabanci mai cike da adalci a Nijeriya maimakon nuna fushin siyasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.

Shugaban marasa rinjaye na Majalisar Wakilai Ali Isah, ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na Majalisar bayan wata ganawa da mai kula da jihar Ribas Sole a Abuja.

 

Ali Isah, ya bayyana cewa mai kula da jihar ta Ribas ya kasance a gidan a wani bangare na ziyarar da ya saba yi domin yiwa kwamitin riko da ke sa ido kan al’amuran gwamnati.

 

Shugaban marasa rinjaye wanda ya jagoranci taron a madadin shugaban kwamitin wanda ya zama shugaban masu rinjaye na majalisar Farfesa Julius Ihonvere, ya bayyana gamsuwa da kokarin da mai gudanarwa shi kadai yake yi na wanzar da zaman lafiya a jihar.

 

Ya ce mai kula da jihar ya tuntubi manyan masu ruwa da tsaki kan rikicin shugabancin jihar Ribas, shugabannin cibiyoyin addini da na gargajiya, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki don ganin an warware matsalar cikin ruwan sanyi domin ci gaban jihar.

 

Sai dai jami’in da ya gabata, ya umurci mai kula da shi kadai da ya tabbatar da cewa rikicin shugabancin jihar Ribas bai shafi biyan albashin ma’aikatan gwamnati da wadanda suka yi ritaya duk wata da fansho ba kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da majalisar dokokin kasar ke yin duk mai yiwuwa don tabbatar da mulkin dimokuradiyya a kasar nan.

 

Ali Isah, ya kuma tabbatar da cewa kwamitin wucin gadi zai ci gaba da tuntubar mai gudanarwa da bangaren zartarwa don hana tsawaita dakatarwar daga wa’adin watanni shida domin samun ci gaba.

 

COV: TSIBIRI

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Kwamatin Tantance Ayyukan Kananan Hukumomi Na Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Isa Sule Tankarkar
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba