Jagora: Amurka Ta Kwana Da Sanin Cewa Ba Wata Riba Da Za Ta Ci Ta Hanyar Yi Wa Iran Barazana
Published: 21st, March 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana cewa; Amurkawa su kwana da sanin cewa, babu wani abu da za su samu, ta hanyar yi wa Iran barazana, kuma waninsu ma ya sani cewa, idan har su ka aikata wani abu maras kyau akan Iran, to za su fuskanci mayar da martani mai tsanani.
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya gabatar da jawabi a yau Juma’a dangane da bikin sabuwar shekara ta Noruz a Husainiyyar Imam Khumaini dake nan Tehran, ya bayyana cewa; Babban kusakuren ‘yan siyasar Amurka da kuma na Turai , shi ne daukar ‘yan gwagwarmaya a wannan yankin da cewa ‘yan koren Iran, da hakan batunci a gare su.”
Jagoran juyin musuluncin na Iran ya kara da cewa; Al’ummar Yemen, kamar sauran ‘yan gwgawarmaya a cikin wannan yankin suna da dalilai na gwgawarmaya, Iran kuwa ba ta da bukatar ‘yan kore.”
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma kara da cewa; “Ko kadan, ba mu ne farau ba acikin wannan rikicin,amma idan wani ya fara aikata wani abu mummuna, to zai fuskanci mayar da martani mai tsanani.
Jagoran juyin musuluncin ya kuma ce; Karshen abinda zai faru da gwgawarmaya shi ne cin kasar abokan gaba ‘yan sahayonoya.
Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniya marasa rahama suke yi,ya sosa zukatan al’ummu musulmi da wadanda ba musulmi ba.
Jagoran juyin musuluncin na Iran ya yi bitar muhimman abubuwan da su ka faru a shekarar da ta gabata ta hijira shamshiyya da su ka hada mai daci da kuma dadi. Daga ciki ya bayyana hatsarin da faru a wurin hako ma’adanai na Tabas, dake arewacin Iran, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 50.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Jagoran juyin
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
Aƙalla mutum huɗu ciki har da jaririn wata tara aka kashe a wani hari da aka kai ƙauyen Nkiendowro da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.
Mutanen da suka rasu sun haɗa da mata biyu da namiji ɗaya, wanda aka ce suna aikin jigilar kwashe tumatir daga ƙauyen zuwa kasuwar Farin-Gada da ke Jos lokacin da aka kai musu hari.
Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a FilatoWasu mutum biyu kuma sun jikkata a harin, wanda yanzu haka suna karɓar magani a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.
Shugaban tsaron al’ummar Miango, Josiah Zongo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an ajiye gawarwakin, yayin da waɗanda suka jikkata ke karɓar kulawa.
Rundunar ’yan sandan Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba kan harin.
A wani lamari makamancin haka, an kai hari ƙauyen Murish da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a daren ranar Laraba, amma matasa da mazauna ƙauyen sun yi nasarar kare kansu daga maharan.
Wani matashi daga ƙauyen ya bayyana cewa maharan sun shigo suna harbi, amma mutanen ƙauyen sun kare kansu.
Shohotden Mathias Ibrahim, Daraktan Al’adu na ƙungiyar Mwaghavul Development Association kuma shugaban sansanin ‘yan gudun hijira a Mangu, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankali su ci gaba da harkokinsu cikin lumana.
Ƙananan hukumomin Mangu da Bassa sun fuskanci hare-hare da dama a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin al’umma game da tsaro a Jihar Filato.