Jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana cewa; Amurkawa su kwana da sanin cewa, babu wani abu da za su samu, ta hanyar yi wa Iran barazana, kuma waninsu ma ya sani cewa, idan har su ka aikata wani abu maras  kyau akan Iran, to za su fuskanci mayar da martani mai tsanani.

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda ya gabatar da jawabi a yau Juma’a dangane da bikin sabuwar shekara ta Noruz a Husainiyyar Imam Khumaini dake nan Tehran, ya bayyana cewa; Babban kusakuren ‘yan siyasar Amurka da kuma na  Turai , shi ne daukar ‘yan gwagwarmaya a wannan yankin da cewa  ‘yan koren Iran, da hakan batunci a gare su.”

Jagoran juyin musuluncin na Iran ya kara da cewa;  Al’ummar Yemen, kamar sauran ‘yan gwgawarmaya a cikin wannan yankin suna da dalilai na gwgawarmaya, Iran kuwa ba ta da bukatar ‘yan kore.”

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma kara da cewa; “Ko kadan, ba mu ne farau ba acikin wannan rikicin,amma idan wani ya fara aikata wani abu mummuna, to zai fuskanci  mayar da martani mai tsanani.

Jagoran juyin musuluncin ya kuma ce; Karshen abinda zai faru da gwgawarmaya shi ne cin kasar abokan gaba ‘yan  sahayonoya.

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma ce; Abinda ‘yan sahayoniya marasa rahama suke yi,ya sosa zukatan al’ummu musulmi da wadanda ba musulmi ba.

Jagoran juyin musuluncin na Iran ya yi bitar muhimman abubuwan da su ka faru a shekarar da ta gabata ta hijira shamshiyya da su ka hada mai daci da kuma dadi. Daga ciki ya bayyana hatsarin da faru a wurin hako ma’adanai na Tabas, dake arewacin Iran, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 50.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Jagoran juyin

এছাড়াও পড়ুন:

Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare

Fitattun dalibai akalla 12 ne  daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare  a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).

A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.

Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.

A cewarsa, an zabo daliban 12 ne  sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.

Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.

“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.

Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.

A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.

Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  •   Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam ” Nahid 2″ Da Zai Samar Wa Yankunan Karkara Hanyar Sadarwa Ta “Internet”
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin