Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira
Published: 21st, March 2025 GMT
Wata gobara da ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Munna Albadawi da ke ƙaramar hukumar Jere a Jihar Borno, ta lalata wasu gidaje 10 tare da salwantar da rayuwar yaro mai shekara 7 mai suna Abubakar Gargar.
A cewar shugaban sansanin, Babangida Mahmud gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 3:00 asubahin safiyar ranar 20 ga watan Maris, 2025, inda gobarar ta laƙume kayayyakin abinci da tufafi da dai sauran kayayyaki.
Wanda kawo yanzu ba a tantance adadin asarar da ta haifar ba baya ga salwantar rai guda.
Hukumar kashe gobara ta Jihar Borno tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro sun yi nasarar shawo kan gobarar da ƙyar da jibin goshi bayan da ta yi ɓarna mai yawan gaske.
Tuni dai aka yi wa marigayin jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya shimfiɗa.
Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar (SEMA) da sauran hukumomin jin ƙai sun baza jami’ansu a sansanonin don daidaita lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan gudun hijira Gobara a Maiduguri Munna Albadawi
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta amince da fara karɓar dalibai a sabbin darussa guda shida a fannin noma a Jami’ar Jihar Gombe (GSU) a shekarar karatun 2025/2026.
Za a gudanar da shirye-shiryen ne a sabuwar Tsangayar Noma da aka kafa a garin Malam Sidi da ke Karamar Hukumar Kwami.
A ranar Litinin bayan taron majalisar gudanarwar jihar, Kwamishinan Noma da Kiwo, Barnabas Malle, ya bayyana cewa an amince da fara aikin sabuwar tsangayar aikin nomar ce ranar 21 ga Watan Mayu, 2025.
Sabbin darussan da aka amince da su sun haɗa da digir a bangaren Noma, Digiri a bangaren Gandun Daji da Dabbobin Jeji, Digiri a Kimiyyar Noma da Digiri a Kimiyyar Kasa, sai Digiri a fannin Tattalin Arzikin Noma.
Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a AlkaleriBarnabas Malle ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ware filin gona mai girman hektar 365 a Garin Tafida da ke Karamar Hukumar Yamaltu Deba, domin bincike da aikin gwaji na ɗalibai.
Ya kara da cewa ana kokarin samun ƙarin fili a Garin Kurugu da ke Karamar Hukumar Kwami, don fadada ayyukan kwalejin a nan gaba.
Kwamishinan Ilimi Mai zurfi, Shettima Gadam, ya kuma tabbatar da cewa NUC ta ba da cikakken izini ga jami’ar don fara daukar daliban ne a wadannan darussa daga shekarar karatun 2025/2026.