HausaTv:
2025-05-01@04:32:28 GMT

 HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke

Published: 21st, March 2025 GMT

Jaridar “Yediot-Ahranot” ta buga wani rahoto da yake kunshe da gargadi daga jami’an sojan mamaya akan yadda ake samun koma baya na sojojin sa-kai saboda da dalilai mabanbanta.

Daga cikin dalilan da jaridar ta bijiro da su da akwai gajiya da yaki na lokacin mai tsawo da HKI ta shiga, sai kuma matsaloli na tattalin arziki da  kashe kudade masu yawa wajen kula da su.

Haka nan kuma manyan jami’an sojan mamayar sun bayyana yiyuwar rusa rundunar sojan sa-kai din saboda babu wadanda su ka dace su jagorance ta,  ga kuma tsadar tafiyar da rundunar kamar yadda jaridar ta “Ahranot” ta bayyana.

Ita kuwa jaridar “Financial-Times” ta bijiro da tata majiyar da take cewa; Yakin da ba shi da ranar karewa da Isra’ila take yi, ya gajiyar da sojojin sa-kai.

Wani sashe na rahoton jaridar ya ambaci cewa; Tare da cewa yarjejeniyar da aka yi da sojojin sa-kai din shi ne cewa a cikin shekara daya za su yi yakin kwanaki 30 ne kadai,amma kuma yanzu an sanar da iyalansu  cewa, su kasance cikin shirin yin yaki babu kakkautawa har na tsawon shekaru masu yawa.

Jaridar ta “Financial Times” ta kuma ce ‘yan sahayoniyar suna da bukatar Karin sojoji 10,000 saboda kara tsaro, a yankunan da suke kusa da Gaza.

HKI tana da cikakkun sojoji170,000 sai kuma sojojin sa-kai da su ka kai 465, a 2024 kamar yadda  shafin :Global Fire Power” ya ambata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030

A cewarsa, wajibi ne shirin ya mayar da hankali kan burin cimma zamanantarwa irin ta gurguzu da nufin gina babbar kasa da samun ci gaba wajen farfado da ita. Shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar, wanda shi ne daftarin dake zaman jigon jagorantar ci gaba na matsakaici da dogon zango a bangaren tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin, yana zayyana baki dayan burikan kasar da manyan ayyuka da manufofin da ake aiwatarwa a dukkan bangarori cikin shekaru 5. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi