HausaTv:
2025-07-08@06:29:39 GMT

 HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke

Published: 21st, March 2025 GMT

Jaridar “Yediot-Ahranot” ta buga wani rahoto da yake kunshe da gargadi daga jami’an sojan mamaya akan yadda ake samun koma baya na sojojin sa-kai saboda da dalilai mabanbanta.

Daga cikin dalilan da jaridar ta bijiro da su da akwai gajiya da yaki na lokacin mai tsawo da HKI ta shiga, sai kuma matsaloli na tattalin arziki da  kashe kudade masu yawa wajen kula da su.

Haka nan kuma manyan jami’an sojan mamayar sun bayyana yiyuwar rusa rundunar sojan sa-kai din saboda babu wadanda su ka dace su jagorance ta,  ga kuma tsadar tafiyar da rundunar kamar yadda jaridar ta “Ahranot” ta bayyana.

Ita kuwa jaridar “Financial-Times” ta bijiro da tata majiyar da take cewa; Yakin da ba shi da ranar karewa da Isra’ila take yi, ya gajiyar da sojojin sa-kai.

Wani sashe na rahoton jaridar ya ambaci cewa; Tare da cewa yarjejeniyar da aka yi da sojojin sa-kai din shi ne cewa a cikin shekara daya za su yi yakin kwanaki 30 ne kadai,amma kuma yanzu an sanar da iyalansu  cewa, su kasance cikin shirin yin yaki babu kakkautawa har na tsawon shekaru masu yawa.

Jaridar ta “Financial Times” ta kuma ce ‘yan sahayoniyar suna da bukatar Karin sojoji 10,000 saboda kara tsaro, a yankunan da suke kusa da Gaza.

HKI tana da cikakkun sojoji170,000 sai kuma sojojin sa-kai da su ka kai 465, a 2024 kamar yadda  shafin :Global Fire Power” ya ambata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Mufti Na Masarautar Oman Ya Yi Kakkausar Suka Kan Masu Son Kulla Alaka Da H.K.Isra’ila

Babban Mufti na masarautar Oman ya yi kakkausar suka kan kasashen da ke neman kulla alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila

Babban Mufti na masarautar Oman, Sheikh Ahmed bin Hamad Al-Khalili, ya bayyana mamakinsa kan yadda wasu kasashe ke son kulla                     alaka da makiya yahudawan sahayoniyya, wata kasa ‘yar mamaya maras tushe.

A cikin wani bayani da ya wallafa a shafinsa na X, Ahmed bin Hamad Al-Khalili ya ce: “Abin mamaki ne yadda wasu kasashe ke son kyautata alaka da makiya yahudawan sahayoniyya, alhali su kansu suna kallon wannan mahalukiya a matsayin wata kasa mai gushewa ko ba dade ko ba jima, al’ummarta dai suna son ci gaba da yakin ne kawai don ci gaba da wanzuwarta, in ba haka ba, babu wanda a can yake son ci gaba da zama a wannan kasa bayan sun ga cewa hakan ba ya cikin maslahar rayuwa.”

Al-Khalili ya ce: “Ta yaya wadanda suke da tushe zasu kulla alaka da gwamnati da zata gushe da hukuma wacce zata gushe ko ba dade ko ba jima.?

Babban Mufti na masarautar Oman ya kara da cewa: “Idan kana son sanin girman bala’i da girman masifa, to ka yi tunanin yadda alakarka zata kasance da mai dabi’ar dabbobi mai kashe fararen hula daga yara da mata da kuma tsofaffi, ta yaya zai kare maka naka hakkokin?  Ya karkare bayanin da cewa: “Mutum ya halaka a cikin kwanakinsa na jarrabawa…idan baya iya bambance tsakanin mai kyau da maras kyau.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
  • Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
  • Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Lardin Hodeidah Na Kasar Yemen
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Babban Mufti Na Masarautar Oman Ya Yi Kakkausar Suka Kan Masu Son Kulla Alaka Da H.K.Isra’ila
  • Jaridar Telegraph: Makaman Iran Masu Linzami Sun Sauka Kai Tsaye Akan  Cibiyoyin Sojan Isra’ila Guda 5  
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari