HausaTv:
2025-07-06@21:55:03 GMT

 HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke

Published: 21st, March 2025 GMT

Jaridar “Yediot-Ahranot” ta buga wani rahoto da yake kunshe da gargadi daga jami’an sojan mamaya akan yadda ake samun koma baya na sojojin sa-kai saboda da dalilai mabanbanta.

Daga cikin dalilan da jaridar ta bijiro da su da akwai gajiya da yaki na lokacin mai tsawo da HKI ta shiga, sai kuma matsaloli na tattalin arziki da  kashe kudade masu yawa wajen kula da su.

Haka nan kuma manyan jami’an sojan mamayar sun bayyana yiyuwar rusa rundunar sojan sa-kai din saboda babu wadanda su ka dace su jagorance ta,  ga kuma tsadar tafiyar da rundunar kamar yadda jaridar ta “Ahranot” ta bayyana.

Ita kuwa jaridar “Financial-Times” ta bijiro da tata majiyar da take cewa; Yakin da ba shi da ranar karewa da Isra’ila take yi, ya gajiyar da sojojin sa-kai.

Wani sashe na rahoton jaridar ya ambaci cewa; Tare da cewa yarjejeniyar da aka yi da sojojin sa-kai din shi ne cewa a cikin shekara daya za su yi yakin kwanaki 30 ne kadai,amma kuma yanzu an sanar da iyalansu  cewa, su kasance cikin shirin yin yaki babu kakkautawa har na tsawon shekaru masu yawa.

Jaridar ta “Financial Times” ta kuma ce ‘yan sahayoniyar suna da bukatar Karin sojoji 10,000 saboda kara tsaro, a yankunan da suke kusa da Gaza.

HKI tana da cikakkun sojoji170,000 sai kuma sojojin sa-kai da su ka kai 465, a 2024 kamar yadda  shafin :Global Fire Power” ya ambata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Nijeriya Na Kewar Gwamnatin Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jaridar Telegraph: Makaman Iran Masu Linzami Sun Sauka Kai Tsaye Akan  Cibiyoyin Sojan Isra’ila Guda 5  
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
  • Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
  • Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
  •  Antonio Guterres Ya Kadu Saboda Mummunan Halin Da Falasdinawan Gaza Suke Ciki
  • ‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
  • ‘Yan Nijeriya Na Kewar Gwamnatin Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi