Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo
Published: 29th, March 2025 GMT
’Yan Sanda sun kama mutum 14 da ake zargi da hannu a kisan matafiya 16 ’yan Arewa a kan titin Uromi zuwa Obajana, a Jihar Edo.
Sufeto-Janar na ’Yan Sanda (IGP), Kayode Egbetokun, ya yi tir da wannan hari, kuma ya bai wa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Hedikwatar Rundunar da ke Abuja, yin bincike.
Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a AbujaBayan faruwar lamarin, rundunar ’yan sandan Jihar Edo, ta tura jami’anta zuwa yankin domin wanzar da zaman lafiya.
Har ila yau, ana ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere.
Kakakin rundunar ’yan sanda, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce Sufeto-Janar ya ba da umarnin a kamo waɗanda ke da hannu a lamarin.
Ya tabbatarwa da al’umma cewa ’yan sanda ba za su yarda da kisan gilla ba, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.
Sufeto-Janar ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu kuma su ba da haɗin kai wajen bincike.
Haka kuma, ya gargaɗi mutane kan ɗaukar doka a hannunsu, tare da tunatar da su cewa mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba laifi ne.
’Yan sanda sun kuma gargaɗi jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu, tare da kiran su da su riƙa kai rahoton duk wani abu da suka gani wanda ba su yarda da shi ga hukumomin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Matafiya Yan Arewa
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato
Aƙalla mutum 41 aka kashe, yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon hare-haren da aka kai wa jama’a daban-daban a Jihar Filato cikin mako guda da ya gabata.
Yankunan da aka kai wa hari sun haɗa da Bassa, Riyom, Bokkos da Ƙaramar Hukumar Mangu.
Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin DuniyaHakazalika, an ruwaito cewa ɗaruruwan mutane sun rasa matsugunansu, an kuma ƙone gidaje da ba a san adadinsu ba.
Ɗaya daga cikin mafi munin hare-haren ya auku ne a ranar 8 ga watan Yuni, a ƙauyen Bauda da ke yankin Langai a Ƙaramar Hukumar Mangu.
’Yan bindiga sun shiga garin da sassafe, inda suka kashe mutum bakwai tare da ƙond gidaje 61, ciki har da cocin COCIN LCC.
A daren ranar, wasu ’yan bindiga sun sake kai hari garin Chinchim da ke yankin Mangu, inda suka kashe mutum takwas.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Mangu, Emmanuel Bala, ya tabbatar da aukuwar hare-haren.
“Mutane na cikin gidajensu lokacin da aka kai musu hari. An fi amfani da wuƙa wajen kashe su. Mutane takwas aka kashe a Chinchim. Kafin nan, mutane bakwai aka kashe a Bwai, kuma mun yi musu jana’iza a ranar Talata.”
Washegari, 9 ga watan Yuni, an sake kai hari a Gyenbwas da ke Langai, inda aka kashe mutum uku, an kuma ƙone gidaje sama da 90 ciki har da ginin JNI.
Mazauna yankin sun bayyana cewa maharan sun sace abinci, shanu, katifu da sauran kayayyaki.
Sakataren Ƙungiyar Gan Allah Fulani Development Association of Nigeria (GAFDAN), Abubakar Garba, ya musanta zargin cewa Fulani ne suka kai hare-haren.
“Ba ma goyon bayan tashin hankali. Mambobinmu masu bin doka ne. Muna kira ga hukumomin tsaro da su gudanar da bincike don gano masu laifi,” in ji shi.
Wannan rikici ya daɗe yana faruwa tsakanin manoma da makiyaya a yankin, inda suke yawan kai wa juna hare-hare, lamarin da ke ƙara haifar da rashin yarda a tsakaninsu.
Wasu na ɗora laifi kan wasu ƙabilu, wanda hakan ke ƙara dagula lamarin.
A ranar 7 ga watan Yuni, an kashe mutum huɗu a ƙauyen Uwok-Ishe da ke Kekkek a Bassa.
Har ila yau, an sake kai hari Riyom, inda aka kashe wani yaro guda ɗaya, wani kuma ya jikkata.
Rahotanni sun ce an kashe wasu makiyaya biyu a Ancher, yayin da a Kwall aka kashe mutum uku, bayab kai wani hari cikin dare.
Duk da waɗannan hare-haren da suka faru a cikin ƙanƙanin lokaci, Gwamnatin Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba.
Har ila yau, babu wani martani daga kakakin rundunar ’yan sandan jihar ko rundunar Operation Safe Haven (OPSH), duk da ƙoƙarin da manema labarai suka yi na jin ta bakinsu.
Masana tsaro sun bayar da shawara kan yadda za a magance matsalar.
Tsohon jami’in ’yan sanda, SP Bulus Ajiji, ya ce: “Rashin haɗin kan al’umma da kuma rashin bayar da bayanai ga jami’an tsaro na daga cikin matsalolin. Wasu jama’a na kare miyagu kai-tsaye ko ba tare da sani ba.”
Masanin zaman lafiya kuma malami a jami’a, Joel Baba Alfa, ya bayar da shawarar matakan da za a ɗauka.
“Ya kamata gwamnati ta kai farmaki wajen da maharan ke ɓuya maimakon jiran suka kawo hari. Kuma a ƙirƙiro rundunar zaman lafiya ta al’umma wacce za ta ƙunshi dukkanin ɓangarorin da ke rikici da juna.”
Ya kuma ƙara da cewa: “Dole a riƙa bayyana gaskiya. Idan shanu sun mutu ko gonaki sun lalace, sai a sanar da jama’a. Haka kuma, kafofin watsa labarai su guji ɗaukar ɓangaranci kan addini ko ƙabila domin kaucewa tayar da rikici.”