Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo
Published: 29th, March 2025 GMT
’Yan Sanda sun kama mutum 14 da ake zargi da hannu a kisan matafiya 16 ’yan Arewa a kan titin Uromi zuwa Obajana, a Jihar Edo.
Sufeto-Janar na ’Yan Sanda (IGP), Kayode Egbetokun, ya yi tir da wannan hari, kuma ya bai wa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Hedikwatar Rundunar da ke Abuja, yin bincike.
Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a AbujaBayan faruwar lamarin, rundunar ’yan sandan Jihar Edo, ta tura jami’anta zuwa yankin domin wanzar da zaman lafiya.
Har ila yau, ana ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere.
Kakakin rundunar ’yan sanda, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce Sufeto-Janar ya ba da umarnin a kamo waɗanda ke da hannu a lamarin.
Ya tabbatarwa da al’umma cewa ’yan sanda ba za su yarda da kisan gilla ba, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.
Sufeto-Janar ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu kuma su ba da haɗin kai wajen bincike.
Haka kuma, ya gargaɗi mutane kan ɗaukar doka a hannunsu, tare da tunatar da su cewa mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba laifi ne.
’Yan sanda sun kuma gargaɗi jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu, tare da kiran su da su riƙa kai rahoton duk wani abu da suka gani wanda ba su yarda da shi ga hukumomin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Matafiya Yan Arewa
এছাড়াও পড়ুন:
Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
Bayo Onanuga, Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, ya ce wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu ne kawai saboda ya fito daga Kudancin Najeriya.
Yayin wata hira da Trust Radio, Onanuga ya ce maganar cewa ana yi wa Arewacin Najeriya wariya ba gaskiya ba ce, face tsantsar siyasa kawai.
Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin TarayyaYa ce ƙorafin da Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), ta yi na cewa an yi watsi da Arewa wajen naɗe-naɗen muƙaman gwamnati da ayyukan ci gaba, wata dabara ce kawai don rage ƙimar shugabancin wanda ya fito daga Kudu.
Ya shawarci ’yan siyasar Arewa da su yi haƙuri, kamar yadda ɓangare Kudu ya yi lokacin mulkin marigayi Muhammadu Buhari, wanda ya shugabanci ƙasar har na tsawon shekaru takwas.
“Shugaba Tinubu ɗan Najeriya ne kamar kowa. Ya cancanci yin shekaru takwas a kan mulki kamar yadda Buhari ya yi. Ka da mu lalata ƙasa saboda son zuciya,” in ji Onanuga.
Dangane da zargin cewa an fi bai wa ’yan Kudu muƙamai, Onanuga ya ce masu sukar Tinubu su kawo hujjoji da ƙididdiga maimakon su ci gaba da yin zargin da ba shi da tushe.
Ya ƙara da cewa babu wani yanki da ba shi da matsalar hanyoyi ko ayyukan da ba a kammala gama ba, amma ya ce gwamnatin yanzu na ƙoƙarin gyara abubuwan da ta gada.
“Kafin ku zargi gwamnati, sai ku binciki gaskiyar lamarin. Wannan duk siyasa ce kawai don a raina Shugaban Ƙasa,” in ji shi.
Onanuga, ya kuma kare matakin da Tinubu ke ɗauka wajen inganta tsaro.
Ya ce an samu ci gaba sosai, inda ya kafa misalin cewar dukkanin shugabannin tsaro daga yankin Arewa suka fito.
Ya ce yanzu yana iya yin tafiya daga Kaduna zuwa Abuja cikin kwanciyar hankali, tafiyar da a da ta ke da hatsari sosai.