Karamar Hukumar Jahun Ta Bada Tallafin Noman Rani Ga Manoma 300
Published: 29th, March 2025 GMT
Majalisar Karamar Hukumar Jahun dake Jihar Jigawa ta kaddamar da rabon tallafin kayan noman rani ga manoma 300.
A jawabinsa wajen bikin da aka gudanar a Garin Darai, shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Jamilu Muhammad Danmalam yace hakan na daga cikin manufofin Gwamna Umar Namadi na bunkasa noman rani da na damina domin kawar da yunwa da kuma samar da abinci ga al’umma.
A cewar sa, karamar Hukumar ta ware wasu yankunan Sahara domin fara noman rani a karo na farko dan fadada harkar noma a kan Tudu.
Alhaji Jamilu Danmalam yace an zabi kauyen Tunubu dake mazabar Kanwa domin fara noman Rani.
Ya kara da cewar, wadanda suka anfana da tallafin za su ci moriyar kaso 60 cikin 100, yayin da zasu dawowa da gwamnati kaso arba’in kacal 40.
A nasa jawabin, jami’in kula da noman rani Malam Suraja Dahiru ya ce gwamnatin Jihar Jigawa ta bada umarnin baiwa matasa filin noma a kalla kadada 100 a kowacce karamar hukuma.
Ya yi nuni da cewar, shugaban karamar Hukumar Jahun ne kadai ya kara adadin filin noma zuwa dari uku.
Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, kayayyakin tallafin da aka raba sun hada da Injin ban ruwa da takin zamani buhu bakwai da irin shuka na shinkafa buhu daya da injin feshi da maganin kwari da sauran kayan aikin gona.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Jahun Noman Rani
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi
Rundunar ’Yan sandan Jihar Kebbi ta cafke wasu mutum huɗu a yankin Kamba da ke jihar, bisa zargin su da shigar da babura uku da suka saya daga Jamhuriyar Benin domin kai wa kungiyar ta’addanci ta Lakurawa.
Haka kuma an kama wani Mubarak Ladan bayan ya yi tayin cin hancin naira dubu dari shida (₦600,000) ga DPO na Kamba, SP Bello Mohammad Lawal, domin a saki waɗanda aka kama.
Kakakin rundunar ’yan sanda ta jihar, CSP Nafiu Abubakar, ya ce baburan da ake kira “Boko Haram” guda uku an saye su ne kan kudi naira miliyan 5 da dubu 400, kuma an tanadar da su ne domin kai wa kungiyar Lakurawa ta hannun wani Alhaji da ke a Kangiwa.
Sanarwar ta ƙara da cewa an cafke mutanen ne bayan samun sahihan bayanai, inda jami’an ’yan sanda tare da ’yan sa-kai ƙarƙashin jagorancin DPO na Kamba suka kai samame
Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya umurci Mataimakin Kwamishina na Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID), Birnin Kebbi, da ya bi sahun sauran waɗanda suka tsere a lamarin