Yawancin wadanda suke da HNd basu samu damar tafiya aikin Yiwa kasa Hidima/Aikin Bautawa kasa wanda hakan ne kuma aka gay a kamata ayi masu adalci kan lamarin

Sai dai kuma irin ci gaban da aka samu ya kawo ko samar da wata matsala ta yadda wadanda suka yi karatun suka kammala a makaranta sai ta kasance wasu daga cikinsu basu samu damar tafiya aikinyiwa kasa hidima ba saboda irin karatun da suka yi.

Da yake bada ta shi gudunmawa darekatan lamurran ‘yan jaridu da hulda da jama’a ma’aikatar ilimi ta tarayya Boriowo Folasade, ya fitar da sanarwa wadda take tabbatar da gaskiyar lamarin na abubuwan da suka biyo bayan dukkan tarurrrukan da kuma ganawar da aka yi.

Sanarwa ta nuna cewa sabon matakin da aka dauka wani abin farincikine ga wadanda suka kammala karatun da ake samun Babbar difiloma ta kasa HNd wadanda a baya ba a basu damar tafiya wuararen da za su yiwa kasa hidima ba.

An ma bayyana cewar matakan da ma’aikatar ilimi ta tarayya ta dauka na tabbatar da cewar ana yin adalci ya kasance ana tafiya da kowa a lamarin ilimi na Nijeriya.

Su ma wadanda suka kammala karatun nasu ba irin na wadanda suka zauna a makaranta ba, suma za su iya je aikin yiwa kasa hidima na shekara daya da takwarorin su wadanda suka samu ko karatun da ya basu damar samun digiri suke yi.

Domin samu daukar mataki wanda ba’a vata lokaci ba an umarci Hukumar kula da ilimin daya shafi fasaha da kere- kere (NBTE)ta gaggauta samar da bayanai na wadanda suka kammala HNd domin tafiya harkar ta yi wa kasa hidama NYSC.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za ta kammala aikin shimfiɗa layin dogo wanda ya taso daga Kaduna zuwa Kano a cikin shekarar 2026 mai zuwa.

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a yau Laraba.

Kazalika, takwaransa na sufuri, Sa’idu Ahmed Alkali ya jaddada hakan ne a yayin jawabinsa a wajen wani taron tuntuɓa tsakanin ’yan ƙasa da gwamnati da ke gudana a Jihar Kaduna.

Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa

A cewar ministan, lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau mulki kashi 15 cikin 10 na aikin kawai aka kammala.

Wata sanarwa da ma’aikatar yaɗa labarai ta fitar ta ambato ministan yana cewa “amma zuwa yanzu an kammala kashi 53 cikin 100.”

A 2024 Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa ta samu rancen kuɗin da za ta kammala aikin daga wani bankin kasuwanci na ƙasar China, abin da ministan ya jaddada a yau ɗin.

Kazalika, ministan ya ce Gwamnatin Tarayyar ta samu duka kuɗin gudanar da aikin gina layin dogo daga birnin Maiduguri na Jihar Borno zuwa garin Aba na Jihar Abiya.

“Layin dogon mai tsawon kilomita 1,443 zai ratsa jihohin Borno, da Yobe, da Gombe, da Bauchi, da Filato, da Kaduna, da Nasarawa, da Binuwai,” in ji sanarwar da kakakin ministan Rabiu Ibrahim ya fitar.

Sai dai sanarwar ba ta bayyana inda gwamnatin ta samo kudin ba.

Ministan ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta gyara layin dogo na dakon kaya tsakanin Legas zuwa Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata