Aminiya:
2025-07-25@05:09:47 GMT

Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga Makka

Published: 2nd, June 2025 GMT

Jami’an Tsaron Saudiyya sun kori mutane sama da 205,000 da ke neman yin aikin Hajji ta barauniyar hanya daga birnin Makka a yayin da aikin Hajjin bana ya kawo jiki.

Daraktan Tsaron Jama’a kuma Shugaban Kwamitin Tsaron Hajji, Laftanar-Janar Mohammed Al-Bassami, ya bayyana cewa hukumomin kasar sun hana mutane sama da 269,000 marasa takardun izini shiga Makka, da kuma motoci 110,000 dauke da mahajjata ba bisa ka’ida ba da aka hana shiga.

An kuma kama 1,239 da suka yi yunkurin jigilar mahajjata ba bisa ka’ida ba, tare da ci tarar masu karya dokokin Hajji sama da 75,000, kuma tare da bankado ofisoshin aikin Hajji na bogi sama da 415.

Laftanar Janar Mohammed Al-Bassami ya sanar da hakan ne a ranar Lahadi, a yayin da yake jawabi game da yadda suka tsaurara matakan taro domin tabbatar da gudanar da aikin Hajjin bana cikin tsari da bin doka.

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta ba makarantu hutun kwana 10 Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne

Jami’in ya jaddada amfani da fasahar zamani don inganta tsare-tsaren tsaro, yana mai da nanata cewa jami’an tsaro suna sanya ido sosai kan duk wani mai karya doka, a kokarinsu na ganin an yin aikin hajjin bana cikin nasara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Saudiyya Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum

Gwamnatin Borno na ci gaba da ƙoƙarin ganin ta samo mafita domin iya biyan sabon albashin ma’aikata kamar yadda aka tsara a matakin ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
  • Jami’an Shige Da Fice Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum
  • Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO
  • Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne