Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
Published: 21st, March 2025 GMT
Ya nemi wadanda har zuwa yanzu ba su dawo da fom dinsu ba da hoto da su gaggauta yin hakan domin su samu biza daga kasar Saudiyya Arabiyya.
Shugaban ya nemi maniyyatan da su bai wa hukumar cikakken hadin kai domin samun nasarar gudanar da aikin hajjin cikin nasara da kwanciyar hankali.
Bayanai sun yi nuni da cewa wadanda suka fara ajiye kudin kujeru amma ba su kammala biya ba su na da zabin ko su amshi kudadensu ko su bari a asusun hukumar har zuwa aikin hajjin badi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
Garkuwan sararin samnaiyar kasar Iran a lardin Zanjan ya bada labarin kakkabo jiragen yakin na HKI guda biyi wadanda ake sarrafasu daga nesa a sararin samaniyar.
Kamfanin dillancin lbaran Tasnim na sojojin kasar Iran ya nakalto majiyar dakarunn juyin juya halin musulunci na kasar Iran tana fadar haka.
Labarin ya kara da cewa rubuce rubucen da aka rubuta a jikin jiragen da aka tarwatsa sun bayyan cewa kirar kasar Amurka ce. Wannan yake tabbatar da irin hannun da Amurka take da shi a cikin yakin da Iran take fafatawa da HKI.
A wani labarin kuma yansandar yanar gizo sun kama mutane biyu wadanda suke yada labaran karya dangane da yaki da kuma shuwagabannin kasar.
Har’ila yau an kama wasu wadanda suke da kayakin hada kananan jirage a cikin gidajensu a lardin albus su tada su don kai hare hare a madadin HKI.