“Amma gwamnoin sun ce a’a. Ba sa son hakan. Sun ce idan kudaden n ya kai ga CBN, ya nuna cewa gwamnatin tarayya ce take kulawa da komi.”

Majiyar ta ce tattaunawar Tinubu da gwamnoni ya bayyana cewa, gwamnonin na bukatar a kai kudaden zuwa bankunan kasuwanci nan take.

“Daya daga cikin gwamnonin ya ce idan har CBN ke kula da asusun, za su bukaci amincewa daga wurin akanta janar na Nijeriya.

Wannan yana nufin cewa har yanzu yana karkashin ikon gwamnatin tarayya ne kuma ba su bukatar hakan ya faru. Suna son a kai shi ga banki na kasuwanci. Amma gwamnatin tarayya ta ki amincewa,” in ji majiyar.

Game da sakamakon ganawar, majiyar ta ce, “Sun ce ganawar ta haifar da da mai ido. Amma ban san abin da suka tsaya a kai ba. Suna aiki tare da wasu ma’aikata don su sami hanyar samun fita. Amma abu mafi muhimmanci shi ne, an rike kudaden kananan hukumomi. Ba a biya ba. Saboda wannan dambarwa.”

A tarihi, an dade ana jayayya kan kudaden kananan hukumomi, musamman domin ikon da ke tsakanin jihohi da kananan hukumomi.
A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta zartar da hukunci mai muhimmanci da ya tabbatar da bai wa dukkan kananan hukumomin kasar nan cin gashin kai.

Ya hukuncin ya bayyana cewa dole ne a biya kudaden kananan hukumomi kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

Wannan ya biyo bayan karar da gwamnatin tarayya ta shigar, wadda ta nemi ta daukaka ‘yancin kananan hukumomi kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya tanada.

Kotun kolin ta jaddada cewa ba ya saba wa tsarin kundin mulki gwamnonin jihohi su ci gaba da kula da kudaden kananan hukumomi, inda ta bukaci a dunga tura wa kananan hukumomin kudadensu kai tsayi daga asusun gwamnatin tarayya.

Haka kuma hukuncin ya hada da tsarin samar da shugabannin kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya ne kawai za su iya samun kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

An samar da wannan tsarin ne don magance yadda gwamnonin jihohi suke nada kwamitocin rikon kwarya ko kuma masu kula da ayyukan kananan hukumomi ba tare da yin zabe ba.

A yanzu haka dai, CBN ya bukaci dukkan kananan hukumomi su mika bayanan asusunsu na tsawan shekaru biyu kafin a fara biyansu.

CBN Ya kuma soma bude asusun banki na kananan hukumomi wanda zai dunga tura musu kudadensu kai tsaye.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnatin tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF

Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF), ta yi korafin cewa Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ta mayar da yankin saniyar ware a kasafin ayyukan raya kasar da take yi a yankin.

Da yake jawabi yayin wani taron tattaunawa da ’yan kasa da Gidauniyar Tunawa da Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna ranar Talata, Shugaban Kwamitin Amintattu na ACF, Alhaji Bashir Dalhatu (Wazirin Dutse), ya yi zargin cewa ana nuna wa yankin bambanci a muhimman manufofin gwamnati da kuma aiwatar da ayyukan raya kasa.

ACF ta ce hakan na faruwa ne duk da irin irin tarin gudunmawar da yankin ya ba gwamnatin mai ci a zaben 2023 da ya gabata.

DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya

Taron dai mai taken: “Nazarin alkawuran zabe: Inganta alakar gwamnati da ’yan kasa domin hadin kan kasa” ya tara gwamnoni da manyan masu rike da mukaman Gwamnatin Tarayya, ciki har da ministoci da sarakunan gargajiya da kuma kungiyoyin fararen hula.

A cewar wadanda suka shirya taron, an shirya shi ne domin karfafa fahimtar juna tsakanin mahukunta da kuma mutane a fadin arewacin Najeriya.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida mana cewa akwai yiwuwar Gwamnatin Tarayya ce ta hada kai da gidauniyar domin a fito da ayyukan gwamnatin a Arewa a daidai lokacin da ake ci gaba da korafin mayar da yankin saniyar ware.

Hakan, a cewar majiyoyin ba zai rasa nasaba da yadda aka ga tarin masu rike da mukamai a gwamnatin da kuma mambobin jam’iyyar APC mai Mulki suka halarci taron ba.

Daga cikin mahalarta taron dai akwai akwai wakilin Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da Mai ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu da kuma Gwamnonin Kaduna (Uba Sani), Gombe (Muhammad Inuwa Yahaya) da Kwara (AbdulRahman AbdulRasaq).

Daga cikin Ministocin da suka sami halartar taron kuwa akwai na Tsaro, Badaru Abubakar, da Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle da na Yada Labarai, Mohammed Idris, da Karamin Ministan Ayyuka, Muhammed Bello Goronyo da Karamin Ministan Gidaje, Yusuf Abdullahi Ata da kuma Karamar Ministar Abuja, Mariya Mahmud Bunkure.

Sauran sun hada da Babban Hafsan Tsaro na Najeriya, Christopher Musa da Babban Hafsan Sojojin Sama, Hassan Abubakar da kuma shugabar hukumar kula da shige da fice ta Najeriya, Kemi Nandap.

Akwai kuma tsofaffin Gwamnoni irin su Ramalan Yero (Kaduna), Aliyu Sjinkafi (Zamfara), Ibrahim Shekarau (Kano) da Mu’azu Babangida Aliyu (Neja) da dai sauransu.

Sai dai ko kafin taron na ranar Talata, ko a makon da ya gabata sai da tsohon Gwamnan Kano kuma dan takarar Shugaban Kas ana jam’iyyar NNPP. Azaben 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi irin wannan zargin cewa gwamnatin Tinubu na fifita kudanci a kan arewaci a fannin ayyukan raya kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka
  • Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Kwamatin Tantance Ayyukan Kananan Hukumomi Na Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Isa Sule Tankarkar
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44