Aminiya:
2025-08-02@12:47:38 GMT

Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu

Published: 21st, March 2025 GMT

Rundunar ‘yan sandan Jihar Legas ta sanar da kama Mista Peter Dike da ake zargi da kashe matarsa ​​a gidansu da ke Unguwar Oke-Ira Ilogbo Eremi, Marogbo.

Rundunar ’yan sandan a ranar Alhamis ta bayyana cewa wanda ake zargin ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa har lahira a lokacin da suka yi ƙazamin faɗa da ya ɓarke a gidan nasu sanadin taƙaddama a ranar Laraba.

’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe Shahararren ɗan kasuwa Nasiru Ahali ya rasu a Kano

Wannan mummunan al’amari ya ƙara dagula al’amuran tashin hankali a cikin gidan ma’aratan da ya kawo sanadin mutuwar matar aure.

A watan Oktoban 2024, an kuma kama Motunrayo Olaniyi da laifin daɓa wa amaryarsa, Olajumoke wuƙa har lahira, a yayin wata hatsaniya mai zafi a gidan su a rukunin gidaje na Amazing Grace Estate, Elepe, a yankin Ikorodu.

Da yake ƙarin haske kan lamarin a ranar Laraba, jami’in hulɗa da jama’a na ’yan sandan, CSP Benjamin Hundeyin, ya bayyana cewa an sanar da jami’an tsaro na sashen Morogbo, kuma ba tare da ɓata lokaci ba suka isa wurin.

Hundeyin ya ci gaba da cewa, “An tabbatar da al’amarin, bayan da jami’an ‘yan sanda da ke sintiri a cikin garin da ke yankin suka samu labarin, sai suka shiga cikin gaggawa suka cafke wanda ake zargin, an samu wuƙar kicin guda ɗaya da tabo da jini daga wajensa, aka kawo shi ofishin aka yi masa tambayoyi.

“Ya amsa laifinsa, an ajiye gawar a ɗakin ajiyar gawa na babban asibitin Badagry, kuma za a miƙa ƙarar zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar, Panti Yaba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Yaba

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum.

Dangane da sanarwar da Amurka ta fitar ta kakaba takunkumi kan jami’an hukumar kare hakkin Falasdinawa da mambobin kungiyar ‘yantar da Falasdinu, Guo Jiakun ya bayyana cewa, Sin ta kadu da hakan, kuma tana nuna takaici da rashin fahimta cewa, Amurka ta yi watsi da kokarin da kasashen duniya ke yi na samar da zaman lafiya ga Falasdinu. Kuma kasar Sin ta dage wajen goyon bayan tsari mai adalci ta al’ummar Falasdinu don maido da halastaccen hakkin al’ummar, kuma za ta ci gaba da yin namijin kokari a wannan fanni tare da sauran kasashen duniya.

Dangane da umarnin da shugaban Amurka Trump ya bayar na kara haraji kan kasashen duniya, Guo Jiakun ya bayyana cewa, matsayin kasar Sin na adawa da cin zarafi na kudaden haraji ba zai canza ba, domin babu wanda zai yi nasara a yakin haraji, kuma ra’ayin amfani da kariyar cinikayya yana cutar da muradun kowane bangare.

Dangane da rahotannin da ke nuni da cewa Amurka ta kaddamar da hare-hare ta yanar gizo kan kasar Sin, Guo Jiakun ya ce, wannan ya fallasa munafuncin Amurkan na koken “kama barawo” a fannin tsaron intanet. Kuma kasar Sin za ta ci gaba da daukar matakan da suka dace don kare tsaron intanet.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa
  • Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
  • PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPP
  • Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya
  • An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
  • Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu