Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa wuƙa ta mutu
Published: 21st, March 2025 GMT
Rundunar ‘yan sandan Jihar Legas ta sanar da kama Mista Peter Dike da ake zargi da kashe matarsa a gidansu da ke Unguwar Oke-Ira Ilogbo Eremi, Marogbo.
Rundunar ’yan sandan a ranar Alhamis ta bayyana cewa wanda ake zargin ya daɓa wa matarsa wuƙa har lahira a lokacin da suka yi ƙazamin faɗa da ya ɓarke a gidan nasu sanadin taƙaddama a ranar Laraba.
Wannan mummunan al’amari ya ƙara dagula al’amuran tashin hankali a cikin gidan ma’aratan da ya kawo sanadin mutuwar matar aure.
A watan Oktoban 2024, an kuma kama Motunrayo Olaniyi da laifin daɓa wa amaryarsa, Olajumoke wuƙa har lahira, a yayin wata hatsaniya mai zafi a gidan su a rukunin gidaje na Amazing Grace Estate, Elepe, a yankin Ikorodu.
Da yake ƙarin haske kan lamarin a ranar Laraba, jami’in hulɗa da jama’a na ’yan sandan, CSP Benjamin Hundeyin, ya bayyana cewa an sanar da jami’an tsaro na sashen Morogbo, kuma ba tare da ɓata lokaci ba suka isa wurin.
Hundeyin ya ci gaba da cewa, “An tabbatar da al’amarin, bayan da jami’an ‘yan sanda da ke sintiri a cikin garin da ke yankin suka samu labarin, sai suka shiga cikin gaggawa suka cafke wanda ake zargin, an samu wuƙar kicin guda ɗaya da tabo da jini daga wajensa, aka kawo shi ofishin aka yi masa tambayoyi.
“Ya amsa laifinsa, an ajiye gawar a ɗakin ajiyar gawa na babban asibitin Badagry, kuma za a miƙa ƙarar zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar, Panti Yaba.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matsayin cin ribar cikakkiyar dimokuraɗiyya ba, duk da cewa an dawo mulkin farar hula shekaru 26 da suka gabata.
Yayin wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Fayemi ya bayyana cewa duk da cewa ana gudanar da zaɓe a kai a kai a ƙasar, har yanzu an rasa muhimman abubuwan da suka kamata su kasance a tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya.
Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna“Bai kamata mu rikita gudanar da zaɓe da aiwatar da dimokuraɗiyya ba,” in ji shi.
“Abin da muka samu a 1999 shi ne ’yancin zaɓar shugabanni, amma hakan kawai ɓangare ne guda ɗaya.
“Abin da muke da shi mulkin farar hula ne, ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba.”
Ya ce an samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnatoci daban-daban tun daga baya, amma har yanzu Najeriya na buƙatar ƙarfafa al’adar dimokuraɗiyya da sauye-sauyen da suka dace.
Fayemi ya kuma tuna da lokacin da ya kasance ɗaya daga cikin masu fafutukar dimokuraɗiyya a zamanin mulkin soja, musamman a lokacin marigayi Janar Sani Abacha.
Ya bayyana yadda suka gudanar da shirye-shirye a wani gidan rediyo a aka ɓoye, don ƙalubalantar gwamnatin soji.
“Ba wai rashin tsoro ba ne, mun san hatsarin da ke tattare da lamarin, amma mun yi imani da abin da muke yi,” in ji shi.
“Na taɓa ɗaukar na’urar watsa shirye-shiryen rediyon Kudirat a cikin jirgin Air France da ya sauka a Legas lokacin da fafutukar ta yi zafi. Wannan kaɗai na iya jefa ni cikin hatsari.”
Ya ce waɗanda suka mutu a lokacin ba don sakaci suka rasa rayukansu ba, sai don sun gaskata ƙudurinsu na ganin an samu ’yanci.
Fayemi ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa karrama wasu daga cikin waɗanda suka fafata wajen dawo da dimokuraɗiyya.
Sai dai ya nuna damuwa cewa wasu da dama da suka taka muhimmiyar rawa a bayan fage ba a karrama su ba.
“Mutane da dama sun sa rayuwarsu cikin hatsari. Su ma sun cancanci a yaba musu.
“Ba daidai ba ne a girmama waɗanda ake gani a manta da waɗanda suka bayar da gudunmawarsu a bayan fage.”
Maganganun Fayemi sun haifar da zazzafar muhawara kan yadda Najeriya ke da buƙatar ci gaba kafin a kira ta da ƙasar da ke da cikakkiyar dimokuraɗiyya.