Aminiya:
2025-05-01@06:27:28 GMT

’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe

Published: 21st, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da wani jami’in Hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) Nathaniel Terwanger Kumashe a ƙauyensa da ke ƙaramar hukumar Tarka a Jihar Benuwe.

An samu rahoton cewa wanda aka yi garkuwan ya taso ne daga Makurdi sansaninsa, domin halartar jana’izar ɗan uwansa da ya rasu a lokacin da aka ɗauke shi zuwa wani wuri da ba a san inda yake ba.

Nasiru Ahali Shahararren masanin masana’antu a Kano ya rasu Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDP

Wani kawun wanda aka yi garkuwan, tsohon mai baiwa gwamnan Jihar Benuwe shawara kan harkokin sufuri, Cif Yimam Aboh, ya shaidawa manema labarai a Makurdi ta wayar tarho cewa an ɗauke jami’in, Insfekta Kumashe a daren Laraba da misalin ƙarfe 10 na dare.

Ya ce, ’yan bindigar sun yi ta harbi don tsoratar da ’yan uwa da maƙwabta kafin su yi awon gaba da wanda suka yi garkuwan daga gidansu da ke Tse Aboh, Uchi-Mbakor a ƙaramar hukumar Tarka.

Ya kuma bayyana cewa, Kumashe ya koma gidansa ne bayan rasuwar ɗan uwansa wanda za a yi jana’izarsa a yau lokacin da masu garkuwar suka farwa gidan.

A halin da ake ciki, jami’ar hulɗa da jama’a ta Hukumar FRSC a Benuwe, Ngozi Ahula, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ƙara da cewa an kai rahoton lamarin ga ’yan sanda.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane jihar Benue

এছাড়াও পড়ুন:

 Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma

Manyan malaman addinin darikar Roman Katolika za su fara Shirin zabar shugaban darikar tasu a fadar Vatican

Adadin manyan malaman addinin masu mukamin “Cardinal” 130 ne za su taru a fadar Vatican, domin su zabi wanda zai maye gurbin Paparoma Farancis da ya rasu.

Sai dai masu kusancin da fadar ta Vatican suna bayyana cewa, da akwai batutuwa da dama da su ka raba kawunan manyan malaman addinin na Roman Katolika da  su ka batun auren jinsi, da rawar da mata za su taka a karkashin inuwar cocin.

Sai dai kuma wani mai sharhi akan abubuwan da su ka shafi cocin, Reese ya bayyana cewa, masu zaben za su mayar da hankali ne akan wanda zai kare ayyukan da mamacin Paparoma Francis ya bari.

Tare da cewa babu kafa ta yin yakin neman zabe a tsakanin masu mukamin na Cardinal, sai dai da akwai wasu siffofi da halaye da ake son gani da wadanda za su iya zama ‘yan takara.

Ana sanar da wanda ya zama sabon Paparoma ne ta hanyar samun kaso 2/3 na kuri’un da manyan masu zaben su ka kada.

A bisa ka’idar cocin, duk wanda aka yi wa wankan tsarki na  ” Baptisma”zai iya zama paparoma,amma  kuma tun daga 1378 ba a zabi wanda bai kai mukamin “Cardinal” ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano