Aminiya:
2025-07-04@01:42:23 GMT

’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe

Published: 21st, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da wani jami’in Hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) Nathaniel Terwanger Kumashe a ƙauyensa da ke ƙaramar hukumar Tarka a Jihar Benuwe.

An samu rahoton cewa wanda aka yi garkuwan ya taso ne daga Makurdi sansaninsa, domin halartar jana’izar ɗan uwansa da ya rasu a lokacin da aka ɗauke shi zuwa wani wuri da ba a san inda yake ba.

Nasiru Ahali Shahararren masanin masana’antu a Kano ya rasu Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDP

Wani kawun wanda aka yi garkuwan, tsohon mai baiwa gwamnan Jihar Benuwe shawara kan harkokin sufuri, Cif Yimam Aboh, ya shaidawa manema labarai a Makurdi ta wayar tarho cewa an ɗauke jami’in, Insfekta Kumashe a daren Laraba da misalin ƙarfe 10 na dare.

Ya ce, ’yan bindigar sun yi ta harbi don tsoratar da ’yan uwa da maƙwabta kafin su yi awon gaba da wanda suka yi garkuwan daga gidansu da ke Tse Aboh, Uchi-Mbakor a ƙaramar hukumar Tarka.

Ya kuma bayyana cewa, Kumashe ya koma gidansa ne bayan rasuwar ɗan uwansa wanda za a yi jana’izarsa a yau lokacin da masu garkuwar suka farwa gidan.

A halin da ake ciki, jami’ar hulɗa da jama’a ta Hukumar FRSC a Benuwe, Ngozi Ahula, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ƙara da cewa an kai rahoton lamarin ga ’yan sanda.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane jihar Benue

এছাড়াও পড়ুন:

 Na’im Kassim: Mamaya Tana Da Ranar Da Za Ta Zo Karshe

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya ce; Tsayin dakar da kungiyar gwagwarmaya ta yi, ya samo asali ne daga koyi da Imam Hussain ( a.s).

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah wanda ya gabatar da jawabi a daren jiya a yayin zaman Ashura, ya kuma kara da cewa; tafarkin Imam Hussain ( a.s) shi ne wanda ya samar da gwarazan mazaje na musamman da shahidai da su ka fuskanci ‘yan mamaya.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce;  Matasan da su ka yi watsi da duniya  su ka shiga fagen jihadi, sun sadaukar da kansu.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce; kungiyar Hizbullah tana a matsayin kare kai ne,domin wannan kasarmu ce, don haka hakkinmu ne mu kare ta.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  •  Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
  • HOTUNA: An yi jana’izar Dantata a Madina
  • Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu
  • Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
  •  Na’im Kassim: Mamaya Tana Da Ranar Da Za Ta Zo Karshe