’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe
Published: 21st, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da wani jami’in Hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) Nathaniel Terwanger Kumashe a ƙauyensa da ke ƙaramar hukumar Tarka a Jihar Benuwe.
An samu rahoton cewa wanda aka yi garkuwan ya taso ne daga Makurdi sansaninsa, domin halartar jana’izar ɗan uwansa da ya rasu a lokacin da aka ɗauke shi zuwa wani wuri da ba a san inda yake ba.
Wani kawun wanda aka yi garkuwan, tsohon mai baiwa gwamnan Jihar Benuwe shawara kan harkokin sufuri, Cif Yimam Aboh, ya shaidawa manema labarai a Makurdi ta wayar tarho cewa an ɗauke jami’in, Insfekta Kumashe a daren Laraba da misalin ƙarfe 10 na dare.
Ya ce, ’yan bindigar sun yi ta harbi don tsoratar da ’yan uwa da maƙwabta kafin su yi awon gaba da wanda suka yi garkuwan daga gidansu da ke Tse Aboh, Uchi-Mbakor a ƙaramar hukumar Tarka.
Ya kuma bayyana cewa, Kumashe ya koma gidansa ne bayan rasuwar ɗan uwansa wanda za a yi jana’izarsa a yau lokacin da masu garkuwar suka farwa gidan.
A halin da ake ciki, jami’ar hulɗa da jama’a ta Hukumar FRSC a Benuwe, Ngozi Ahula, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ƙara da cewa an kai rahoton lamarin ga ’yan sanda.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane jihar Benue
এছাড়াও পড়ুন:
Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
Hukumar Tattara Haraji ta Ƙasa (FIRS) ta ce ma’aikatanta hudu sun mutu a gobarar da ta tashi a ginin Afriland Towers da ke titin Broad da ke Legas, a ranar Talata.
Aminiya ta rawaito yadda gobara ta mamaye ginin da ke dauke da banki, hukumomi da wasu kamfanoni.
Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Laraba, mai magana da yawun Shugaban FIRS, Zaach Adedeji, wato Dare Adekanmbi, ya ce hukumar na cikin jimami da alhini kan rasuwar ma’aikatan nata.
Sanarwar ta ce, “Cike da alhini da bakin ciki, FIRS na sanar da rasuwar ma’aikatanta hudu a gobarar da ta tashi a ginin Afriland Towers da ke titin Broad, Legas, a ranar Talata. FIRS na daya daga cikin masu haya a ginin, inda Ofishin Binciken Matsakaicin Haraji da Ofishin Haraji na Onikan ke a bene na shida da na bakwai.”
“Jami’an tsaro da na kula da lafiya na hukumar sun gaggauta tuntubar hukumar kashe gobara lokacin da aka sanar da su. Amma da suka isa wurin, hayaki mai kauri da duhu ya turnuke ginin.”
“Hukumar da dukkan ma’aikatanta na cikin alhini kan wannan lamari. Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda suka rasu, kuma muna tare da su a wannan lokaci mai wahala. Za mu ba su dukkan goyon baya da tallafi da ake bukata.”
“Muna aiki tare da dukkan hukumomin da suka dace a Legas domin gano musabbabin wannan mummunan al’amari. A yayin da ake ci gaba da bincike, za mu duba matakan kiyaye lafiyar dukkan ofisoshin FIRS da ke fadin ƙasa, ko na haya ne ko wanda ta mallaka.”