Aminiya:
2025-07-30@21:48:07 GMT

Nasiru Ahali Shahararren masanin masana’antu a Kano ya rasu

Published: 21st, March 2025 GMT

Allah Ya yi wa Alhaji Nasiru Ahali, Shugaban Kamfanin Mainasara & Sons, rasuwa.

Marigayin wanda yake shahararren masanin masana’antu ne ya rasu yana da shekara 108.

Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDP

A cewar majiyoyin na kusa da iyalan marigayin ɗan kasuwar ya rasu ne a wani asibiti da ke Kano a daren ranar Alhamis.

Ana girmama Ahali a matsayin ɗaya daga cikin jiga-jigan masanin asalin masana’antu a Kano. Ya yi ƙoƙari ya kafa tsarin kasuwanci na yau da kullun.

A tattaunawarsa da Daily Trust a shekarar 2018, marigayi Ahli ya bayyana cewa sana’arsa ta haɗa da buga littattafai, bugu takardu, masana’antar bulo, sana’ar fasa dutse, shigo da kaya, kwangilar gama-gari, bunƙasa kadarorin rukunin gidaje, ayyukan ƙarafa da sauransu.

A saƙon ta’aziyyar da ya aike wa iyalan marigayin ta hannun Babban Daraktan Yaɗa Labarai na Gidan Gwamnatin Kano, Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa, Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ba ga iyalansa kaɗai ba, har da jiha da ƙasa da sauran al’ummar Musulmi baki ɗaya.

Ya bayyana marigayin a matsayin ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa masana’antu, inda ya ce shi ne ya tsara tattalin arzikin jihar tare da taka muhimmiyar rawa a tsakanin ƙananan masana’antu da manyan masana’antu a jihar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi

Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Sarkin Karaye, Mai Martaba Alhaji Muhammad Mahraz Karaye, ya kammala rahoton aikinsa na wucin gadi.

 

Darakta Janar na Hukumar, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ne ya bayyana hakan a fadar Sarkin da ke Karaye.

 

Ya ce rahoton ya ƙunshi dukkan abubuwan da suka shafi aikin Hajji tun daga lokacin da aka ƙaddamar da kwamitin a birnin Makkah, ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Kano, Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf.

 

“Rahoton ya kunshi cikakken bayani kan ayyukan da kwamitin ya gudanar zuwa yanzu, kuma zai kasance muhimmin ɓangare na rahoton ƙarshe da za a miƙa ga Gwamna,” In ji shi.

 

Alhaji Lamin Rabi’u ya bayyana cewa Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta rigaya ta tattara nata cikakken rahoton, wanda za a mika wa Gwamnan nan ba da daɗewa ba.

 

A nasa jawabin, Sarkin Karaye ya nuna godiya ƙwarai ga Gwamnan Jihar bisa amincewa da baiwa kwamitin damar gudanar da wannan aiki mai muhimmanci.

 

Shugaban Hukumar gudanarwa na hukumar  Alhaji Yusif Lawan, ya bayyana godiya ga Sarkin Karaye bisa sadaukarwa da haɗin kai da ya bayar, wanda ya taimaka wajen samun nasarar aikin kwamitin.

 

Abdullahi Jalaluddeen

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe
  • Arewa za ta kayar da Tinubu a zaɓen 2027 —Babachir
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya
  • Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya