Jami’ar FUDAMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
Published: 17th, May 2025 GMT
Farfesa Radda ya ce an cire ‘yan takara masu yawa da suka cencenta saboda rashin adalci, duba da cewa sun cika dukkan sharadan da ya dace wajen neman mukamin shugabancin makarantar.
Haka kuma, Farfesa Bichi ya ce zargin da ake masa ba gaskiya ba ne, yana mai cewa an gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci kamar yadda doka ta tanada.
Dukkan ‘yan takarar sun bayyana gamsuwarsu kan shigowar gwamnatin tarayya cikin lamarin, inda suke yi kira ga ministan ilimi ya sake duba dukkan matakan da da aka bi domin yin gaskiya kamar yadda dokar makarantar ta tanada.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe
Rundunar ‘yansanda a jihar Gombe ta umurci rufe duk wata tashar sauka ko daukar fasinjoji a cikin garin Gombe ciki har da fitacciyar tashar Dadin Kowa, inda ta ce, tashar Ibrahim Hassan Dan-Kwambo ce kadai halastacciya.
Bugu da kari, motocin haya da ke dauke da amintaccen launin kala na gwamnati a cikin garin Gombe ne kadai suke da izinin zirga-zirgar daukar fasinjoji a birnin.
Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar SinWannan umarni na kunshe ne acikin wata sanarwar manema labarai da jami’in hulda da jama’a na rundunar a jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, a ranar Litinin, 2 ga watan Yunin 2025.
“An dauki wannan matakin ne daidai da kudurin gwamnati na maido da bin doka, inganta tsaro, da kuma tabbatar da lafiyar fasinjoji. An umurci dukkan masu sana’ar tuki na kasuwanci da su gudanar da dukkan ayyukan lodi da sauke kaya a tashar motoci ta Ibrahim Hassan Dan-kwambo kadai da ke babban birnin jihar.
“Duk wani wanda aka samu ya taka doka zai fuskanci tsauraran sakamako na shari’a, gami da kamawa, gurfanar da shi, da yuwuwar kama motarsa.” In Ji DSP Abdullahi
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp