Asusun kula da kananan yara “UNICEF” na Majalisar Dinkin Duniya ya sanar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe yara 45 a Gaza cikin kwanaki biyu kacal

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bayyana cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe kananan yara 45 a Zirin Gaza a cikin kwanaki biyun da suka gabata, kuma wani abin tunatarwa shi ne cewa: Yara a Gaza na shan wahala da farko, suna fama da yunwa kowace rana kuma suna fuskantar hare-haren wuce gona da iri da muggan makamai kan mai uwa da wabi.

A cikin wata sanarwa da Asusun ya fitar a ranar Juma’a, ya jaddada yi kira da a kawo karshen wahalhalu da kashe-kashen yara a kullum.

A nata bangare, Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa: “Hare-haren sojojin gwamnatin mamayar Isra’ila na ci gaba da yin mummunan tasiri ga cibiyoyin kiwon lafiya, ciki har da asibitin Turai na Gaza da ke Khan Yunis, wanda yanzu ya daina aiki.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya ce kasa ta 12 mafi talauci a duniya — IMF

Wani sabon rahoto da Asusun Bayar da Lamuni IMF ya fitar ya ce Nijeriya na mataki na 12 a cikin jerin kasashe mafiya talauci a fadin duniya.

IMF ya ce talauci na kara karuwa a cikin kasar da ta dauki shekaru biyu tana kokarin sauya fuskar tattalin arziki, amma kuma take dada fadawa cikin duhu na tattalin arziki.

Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan  HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Aminu Ɗantata a Kano

Jaridar Cable ta ruwaito cewa, Nijeriya tana mataki na 12 a cikin kasashe mafiya talauci bisa la’akari da karfin tattalin arziki a ma’aunin GDP na Dalar Amurka 807 a bana.

Kawo yanzu dai shekaru biyu bayan kaddamar da jerin sauye-sauye ga tattalin arziki, amma daga dukkan alamu Nijerya na dada fadawa cikin matsalar talauci idan aka yi la’akari da kasashe 189 da IMF ya gudanar da bincike a cikinsu.

A cikin kasashe 189 da aka gudanar da bincike a cikinsu, Najeriyar na a mataki na 178, inda ta zarta kasashe irin su Yemen da Sudan ta Kudu da Kwango da Nijar da Sudan, wadanda kusan dukkaninsu ke fama da rigingimu a halin yanzu.

Ana kallon sabon rahoton a matsayin alamun kasawa a bangare na masu mulkin Nijeriya da ke fadin cewar suna da burin ceto kasar da ke kara samun nakasu, kamar yadda Ibrahim Shehu, sakataren kungiyar inganta tattalin arzikin arewacin Najeriya ya bayyana.

Akalla Naira tiriliyan 21 ne ake jin matakan gwamnatin kasar guda uku sun samu daga zare tallafin man fetur a shekaru guda biyu.

Ko bayan wasu Naira Tiriliyan 96 da masu mulkin na Abuja suka karba da sunan bashi, akwai Naira tiriliyan guda a shekara da masu mulkin ke samu sakamakon ragin tallafi bisa kudin wuta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Laftanar Kanar Shikarci: Sojojin Iran Suna Cikin Shirin Ko-Ta-Kwana Fiye Da Kowane Lokaci
  • An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Yin Kutse Cikin Yankunan Kasar Siriya
  • Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
  • Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza
  • Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan
  • Nijeriya ce kasa ta 12 mafi talauci a duniya — IMF