UNICEF Ya Ce; Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara 45 Cikin Kwana Biyu Kacal A Gaza
Published: 17th, May 2025 GMT
Asusun kula da kananan yara “UNICEF” na Majalisar Dinkin Duniya ya sanar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe yara 45 a Gaza cikin kwanaki biyu kacal
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bayyana cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe kananan yara 45 a Zirin Gaza a cikin kwanaki biyun da suka gabata, kuma wani abin tunatarwa shi ne cewa: Yara a Gaza na shan wahala da farko, suna fama da yunwa kowace rana kuma suna fuskantar hare-haren wuce gona da iri da muggan makamai kan mai uwa da wabi.
A cikin wata sanarwa da Asusun ya fitar a ranar Juma’a, ya jaddada yi kira da a kawo karshen wahalhalu da kashe-kashen yara a kullum.
A nata bangare, Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa: “Hare-haren sojojin gwamnatin mamayar Isra’ila na ci gaba da yin mummunan tasiri ga cibiyoyin kiwon lafiya, ciki har da asibitin Turai na Gaza da ke Khan Yunis, wanda yanzu ya daina aiki.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno
Dubban mazauna garin Kirawa da ke jihar Borno da mayakan Boko Haram suka raba da gidajensu, sun ce yanzu kullum a kasar Kamaru suke saboda gudun harin ’yan Boko Haram cikin dare.
Mutanen, wadanda yanzu haka ke samun mafaka a kauyukan kasar ta Kamaru, sun kuma koka da halin kuncin da suke ciki a yanzu.
‘Zan iya shiga mummunan yanayi idan Dangote bai aure ni ba’ Lafiyar Tinubu kalau – SoludoMazauna yankin shin shaida wa wata kafar yada labarai a ranar Talata cewa tun bayan harin da aka kai ranar Asabar da ya kai ga janye sojoji daga yankin mazauna kauyuka da dama sun bazu a kauyukan da ke kan iyaka da Kamaru.
Sun kuma ce a sakamakon haka, suna kwana a kan tituna, masallatai da azuzuwan makaranta saboda fargabar hare-hare cikin tsakar dare.
Hakimin yankin na Kirawa, Abdulrahman Abubakar, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya yi kira ga gwamnati da ta gaggauta daukar matakin tsugunar da al’umma da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.
“A halin da ake ciki yanzu ba ma iya yin barci da idanunmu biyu a rufe, yayin da mutanenmu a yanzu ke ke kai kawo a tsakanin kasashen biyu, suna kwana a Kamaru da daddare su yini kuma a Najeriya.
“Wannan shi ne karo na farko da muke fuskantar wannan hari tun bayan da aka sake tsugunar da al’ummarmu shekaru da suka wuce,” in ji Abubakar.
Daya daga cikin ‘yan gudun hijirar, Buba Aji, wanda ya ba da labarin abubuwan da ‘yan Najeriya suka fuskanta a kauyukan Kamaru, ya bayyana hakan a matsayin abin tada hankali da rashin mutuntawa.
Ya ce, “A cikin dare, abubuwan da suka faru yawanci ba su da kyau, misali, a ranar litinin da daddare, an yi ruwan sama kamar da bakin qwarya, wanda yawancin mutanen mu suka kwana ruwan saman na dukan su a filin Allah ta’ala illa kalilan daga cikin mu da muka samu mafaka a masallatai da makarantu, saboda muna fargabar ‘yan tada ƙayar bayan su dawo da dare.
“Yanzu wurin da muke samun mafaka shine Kerawa da Lamise a Kamaru, kuma a kan tituna kai tsaye akasarin mu ke kwana, “ in ji shi.
Ya kara da cewa “A halin yanzu babu wani sojan Najeriya a cikin yankinmj, ‘yan sibiliyan JTF, wadanda sojojin Kamaru ne suma sun koma kasarsu.
“Don haka muna bukatar gwamnati ta saurari kokenmu, ta kuma kawo mana xauki kafin wadannan mutane (masu tada qayar baya) su sake kawo wani harin,“ Buba Aji.