Asusun kula da kananan yara “UNICEF” na Majalisar Dinkin Duniya ya sanar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe yara 45 a Gaza cikin kwanaki biyu kacal

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bayyana cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe kananan yara 45 a Zirin Gaza a cikin kwanaki biyun da suka gabata, kuma wani abin tunatarwa shi ne cewa: Yara a Gaza na shan wahala da farko, suna fama da yunwa kowace rana kuma suna fuskantar hare-haren wuce gona da iri da muggan makamai kan mai uwa da wabi.

A cikin wata sanarwa da Asusun ya fitar a ranar Juma’a, ya jaddada yi kira da a kawo karshen wahalhalu da kashe-kashen yara a kullum.

A nata bangare, Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa: “Hare-haren sojojin gwamnatin mamayar Isra’ila na ci gaba da yin mummunan tasiri ga cibiyoyin kiwon lafiya, ciki har da asibitin Turai na Gaza da ke Khan Yunis, wanda yanzu ya daina aiki.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Shirya Zanga-Zangar Goyon Bayan Halaccin Yunkurin ‘Yantar Da Kasarsu Daga Mamayar Yahudawa

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta shirya wata zanga-zanga da Falasdinawa ke jaddada cewa: babu halacci ga ‘yan mamaya kuma al’ummar Falastinu za su ci gaba da gwagwarmaya

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta jaddada cewa: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba ta da halacci ko kuma wani ikon mallakar wani yanki na Falasdinu da ta mamaye, kuma al’ummar Falastinu za su ci gaba da kare kansu ta hanyar gudanar da gwagwarmaya har sai sun kwato dukkanin Falastinu tare da kafa kasar Falasdinu mai cikakken ‘yanci kai wacce Qudus zata kasance a matsayin babban birninta.

A yayin bikin cika shekaru 77 da kafuwar Nakba, -boren Falasdinawa na farko- kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta bayyana cewa: “Ba za a yi wani sabon Nakba ko sake tilastawa Falasdinawa gudun hijira ba, hadin kan al’umma da gwagwarmaya zasu dakile duk wani makircin makiya, kuma zasu ci gaba da kalubalantar duk wani makirci, domin hakan ne zai karya lagon ‘yan mamaya da tabbatar da samun ‘yanci da komowar ‘yan gudun hijira kasarsu ta gado.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno
  • Isra’ila ta yi barazanar kashe shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen
  • Kudaden da sojojin Afirka suka kashe a bara ya karu da dala biliyan 52 a shekarar 2024
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 143 A Ranar Tunawa Da Musibar Nakba
  • Kungiyar Hamas Ta Shirya Zanga-Zangar Goyon Bayan Halaccin Yunkurin ‘Yantar Da Kasarsu Daga Mamayar Yahudawa
  • Human Rights Watch : Katange Gaza mataki ne na share al’umma
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Gaza
  • Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe