Rikici Tsakanin Faransa Da Aljeriya Ya Shiga Wani Sabon Salo Na Koran ‘Yan Kasashen Juna Daga Kasashensu
Published: 17th, May 2025 GMT
An samu bullar rikicin da ba a taba ganin irinsa ba a dangantaka tsakanin Aljeriya da Faransa
Rikicin ma’aikatan harkokin diflomasiyya tsakanin Aljeriya da Faransa ya dawo kan gaba a fagen dakaddamar da ke tsakaninsu.
Rikici dai na kara kamari ne tsakanin Aljeriya da Faransa, tun daga rikicin korar ‘yan kasar Aljeriya daga Faransa zuwa rikicin korar ma’aikatan diflomasiyyar Faransa daga Aljeriya.
Wannan kiran ya biyo bayan maimaita cin zarafi mai tsanani da bangaren Faransa ya yi ne, yana wakiltar keta doka da aka kafa da kuma keta tsarin al’ada don nada ma’aikata a ofisoshin diflomasiyya da na ofishin jakadancin Faransa da aka amince da su a Aljeriya.
Akalla ma’aikatan Faransa 15 ne aka nada don gudanar da ayyukan diflomasiyya ko na ofishin jakadancin a kasar Aljeriya, ba tare da bin ka’idojin da suka dace ba, gami da sanarwa a hukumance ko kuma ba da izini, kamar yadda ka’idoji da yarjejeniyoyin kasa da kasa suka bukata.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Aljeriya da
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da E3 sun kuduri aniyar bin hanyoyin diflomasiyya dangane da shirin nukiliyar Iran
Iran da kasashen turan nan guda uku sun da ake wa lakabi da E3 sun kudiri anniyar bin hanyoyin diflomasiyya dangane da shirin nukiliyar kasar ta Iran.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin shari’a da kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya bayyana cewa, Iran da kasashen Turan uku Birtaniya da Faransa da Jamus (EU-3) sun kuduri aniyar yin amfani da diflomasiyya dangane da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
Gharibabadi ya bayyana hakan ne a shafinsa na X bayan ganawarsa da wakilan kasashen Turan uku na yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015 a birnin Istanbul na kasar Turkiyya.
Mataimakin ministan harkokin wajen Iran mai kula da harkokin siyasa Majid Takht-Ravanchi shi ma ya halarci taron.
Ya ce, wakilan Iran da daraktocin siyasa na EU-3 sun yi musayar ra’ayi tare da tattauna halin da ake ciki na shawarwarin nukiliya tsakanin Iran da Amurka da kuma dage takunkumin da aka kakaba mata.
Ya ce Iran da EU-3 za su sake haduwa, idan akwai bukata, don ci gaba da tattaunawa.