Rikici Tsakanin Faransa Da Aljeriya Ya Shiga Wani Sabon Salo Na Koran ‘Yan Kasashen Juna Daga Kasashensu
Published: 17th, May 2025 GMT
An samu bullar rikicin da ba a taba ganin irinsa ba a dangantaka tsakanin Aljeriya da Faransa
Rikicin ma’aikatan harkokin diflomasiyya tsakanin Aljeriya da Faransa ya dawo kan gaba a fagen dakaddamar da ke tsakaninsu.
Rikici dai na kara kamari ne tsakanin Aljeriya da Faransa, tun daga rikicin korar ‘yan kasar Aljeriya daga Faransa zuwa rikicin korar ma’aikatan diflomasiyyar Faransa daga Aljeriya.
Wannan kiran ya biyo bayan maimaita cin zarafi mai tsanani da bangaren Faransa ya yi ne, yana wakiltar keta doka da aka kafa da kuma keta tsarin al’ada don nada ma’aikata a ofisoshin diflomasiyya da na ofishin jakadancin Faransa da aka amince da su a Aljeriya.
Akalla ma’aikatan Faransa 15 ne aka nada don gudanar da ayyukan diflomasiyya ko na ofishin jakadancin a kasar Aljeriya, ba tare da bin ka’idojin da suka dace ba, gami da sanarwa a hukumance ko kuma ba da izini, kamar yadda ka’idoji da yarjejeniyoyin kasa da kasa suka bukata.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Aljeriya da
এছাড়াও পড়ুন:
MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122
Hukumar dake kula da ‘yan hijira dake karkashin MDD ta sanar da cewa, mutanen yake-yake da rikice-su ka tilastawa yin hijira a duniya ya kai miliyan 122.
A yau Alhamis ne dai hukumar dake kula da ‘yan hijirar ta bayyana haka, tana kai kara da cewa; gajiyawar da aka yi na warware fadace-fadace da rikicen da suke faruwa a duniya ne su ka kara yawan ‘yan hijirar, daga ciki har da kasashen Sudan da kuma Ukiraniya.
Haka nan kuma ta ce; Tun daga 2015 ne ake samun koma baya na kudaden da ya kamata a rika bayarwa domin taimakawa ‘yan hijira.
Shugaban hukumar ‘yan hijirar ta MDD Filippo Grandi wanda ya gabatar da rahoto akan halin da ake ciki, ya yi ishara da cewa, tun daga watan Aprilu na wannan shekara ta 2025 da ake ciki an sami karuwar mutane miliyan biyu da su ka zama ‘yan hijira, duk da cewa wani adadin da ya kai mutane miliyan biyu ‘yan kasar Syria sun koma kasarsu bayan faduwar gwamnatin Basshar Asad.
Filippo Grandi ya ce rikice-rikicen kasar Myanmar, da yakin Ukiraniya da Sudan su ne ummul-haba’isin karuwar ‘yan hijirar da kuma gajiyawa wajen kawo karshen hakan.
Kasar Amurka tana cikin wadanda su ka rage yawan taimakon kudaden da suke bayarwa a harkar agaji, yayin da kasashe kamar Birtaniya da wasu kasashen turai suke bayar da kadan.