Aminiya:
2025-05-30@11:44:30 GMT

Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda

Published: 25th, February 2025 GMT

Wani dan kwallon Najeriya mai suna Abubakar Lawal daga Jihar Sakkwato ya rasu bayan fadowa daga bane a kasar Uganda, inda yake taka leda.

Rahotanni sun bayyana cewa Abubakar Lawal mai shekaru 29 ya gamu da ajalinsa ne bayan ya fado daga hawa na uku na wanin babban kantin sayar da kayayyaki a Kampala, babban birnin kasar Uganda.

Rasuwar tasa ta haifar haifar da ce-ce-ku-ce a kasar, kamar yadda kafofin yada labarai suka ruwaito. Da farko an alakanta rasuwar tasa da hatsarin babur, kafin daga bisani jami’an tsaro su bayyana cewa ya fado ne daga bene.

Marigayin dan wasan gaba ne a kungiyar kwallon kafa ta Vipers da ke kasar, inda ya fara wasa tun shekara 2022, kafin nan ya shekara biyu yana taka lelda a kungiyar AS Kigali da ke kasar Rwanda.

Kungiyar Vipers ta sanar Abubakar ya rasu ne a ranar Litinin bayan da ya fado daga hawa na uku da kataferen kantin mai suna Voicemall Shopping Arcade a Kampala.

A sakon ta’aziyyarta, kungiyar ta bayyaan marigayin a matsayin, “mutumin kirki mai kyakkyawar zuciya, mai yawan kyauta ne da kuma taimaka wa jama’a,” kamar yadda ya wallafa a shafinta na X.

Runudar ’yan sandan ta sanar da fara bincike kan musabbabin mutuwar dan kwallon na Najeriya.

Hukumar ’yan sandan Uganda ta bayyana cewa dan wasan ya gamu da ajalinsa ne a lokain da ya kai wa wata kawarsa ’yar kasar Tanzaniya ziyara a rukunin ginin.

A sakon ta’aziyyar dan wasan, kungiyar Nasarawa United, tsohuwar kungiyar Abubakar, ta ce, “Muna jimaminin mutuwar fuju’ar tsohon dan wasanmu Abubakar Lawal, kuma muna rokon Allah Ya sada shi da rahama.”

Shi kuwa Mustafa Kizza, dan wasan Uganda, ya ce: “Rashin Lawal abu ne mai wuyar jurewa. Mutumin kirki ne mai fara da hazaka da ba za mu taba mantawa da shi ba.”

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Red Crescent ta Iran da Red Cross ta Saliyo sun cimma yarjejeniyoyi da dama a tsakaninsu

Kungiyar agaji ta red crescent ta iran da kuma kungiyar red cross ta kasar Saliyo sun cimma yarjeniyoyi da dama a tsakaninsu.

An cimma wannan ne a yayin ziyarar da babban daraktan kula da lafiya na kungiyar agaji ta Red Crescent na Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya kai Saliyo tare da gudanar da tarurruka da dama da shugaban kungiyar agaji ta Red Cross ta kasar.

Bayan taron, an rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa tsakanin kungiyar agaji ta Red Crescent ta Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kungiyar agaji ta Red Cross ta Saliyo a ofishin jakadancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da ke Saliyo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Yaya Girman Matsalar Rashin Tsaro A Shekaru Biyun Tinubu?
  • Kasar Iran, Da Kasashen Kungiyar BRICS Sun Gudanar Da Taro Kan Harkokin Tsaro A Mosco
  • OPEC+ Ta Fara Shirin Ayyana Yawan Man Fetur Da Zata Haka Zuwa Sekara Ta 2027
  • Kungiyar ASEAN Ta Bayyana Damuwarta Da Kissan Kiyashi A gaza
  • NEJERIYA A YAU: Sai Yaushe ’Yan Najeriya Za Su Ci Gajiyar Manufofin Shugaba Tinubu?
  • ’Yar Najeriya ta tsinci miliyan 8.2 a Saudiyya ta mayar wa da mai su
  • Red Crescent ta Iran da Red Cross ta Saliyo sun cimma yarjejeniyoyi da dama a tsakaninsu
  • Kungiyar Amnesty Tana Zargin : Gwamantin DRC Da Kungiyar M23 Da Yiyuwar Aikata Lafukan Yaki
  • DAGA LARABA: “Sai Na Tara Kudin Cin Abinci Na Nake Iya Siyan Audugar Al’ada”
  • Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah