HausaTv:
2025-06-19@19:15:34 GMT

IRGC : Jana’izar Nasrallah Wani Sakon ‘yan Gwagwarmaya A Duniya Baki Daya

Published: 25th, February 2025 GMT

Rundinar kare juyin juya halin musulinci ta Iran, ta bayyana bikin jana’izar sakataren kungiyar Hezbollah ta Lebanon mai rasuwa Sayyed Hassan Nasrallah da kuma Sayyed Safiedinne da aka gudanar a matsayin wani babban sako na ‘yan gwagwarmaya ga duniya baki daya.

Wannan babban taron da akayi a Beirut abun tarihi ne ga duniyar musulmi, ya kuma nuna cewa kungiyar Hizbullah, na da karfinta da kuma akidar kyamar sahyoniyawan.

Sanarwar ta kara da cewa: “Bikin da ya samu halartar miliyoyin mutane, a daidai lokacin da ake barazana da jiragen yakin Isra’ila, ya zama wata alama ta karfin Musulunci da cikakken hadin kan al’ummar kasar Labanon.

Sanarwar ta yi nuni da cewa, gagarumin taron makoki daga kasashe daban-daban, addinai da kabilu, da jam’iyyun siyasa, sun sabunta mubaya’a ga shahidan ‘yan gwagwarmayar, tare da bayar da martani mai karfi ga makiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dortmund ta yi canjaras da Fluminense a Club World Cup

Borussia Dortmund ta soma buɗe wasanninta na gasar FIFA Club World Cup da canjaras a karon-battar da ta yi da kungiyar Fluminense ta Brazil a ranar Talata.

Ana dai ganin babbar kungiyar da ta zama gagarabadau a Rio de Janeiro Fluminense a matsayin mafi hatsari a rukunin F wanda ya kunshi har da kungiyar Ulsan HD ta Koriya ta Kudu.

Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump

An dai rika kai wa juna hari a yayin wasan da suka barje gumi a filin wasa na Metlife da ke East Rutherford a wajen birnin New York, sai dai mai tsaron ragar Dortmund, Gregor Kobel ya ceci kungiyarsa bayan wata kwallo da Jhon Arias ya nano masa daga nesa tun kafin tafiya hutun rabin lokaci.

Fluminense wadda tsohon dan wasan PSG da Chelsea, Thiago Silva mai shekaru 40 shi ne kyaftin dinta, ta yi kokarin samun damar Dortmund ana tsaka da kai ruwa na bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, amma Kobel ya rike kwallon da Agustin Canobbio ya yi yunkurin tarar numfashinsa.

Golan dai ya sake yin wata bajintar bayan ya tare kwallon da Everaldo ya yi sakada masa a kusurwar kasa, lamarin da haka a karkare wasan babu ci.

Fluminense dai ta samu gurbin zuwa gasar Club World Cup ta bana bayan nasarar lashe Copa Libertadores da ta yi a shekarar 2023.

Bajintar da Fluminense ta yi a karon-battar ta da manyan kungiyoyin da suka kasance zakaran gwajin dafi a nahiyyar Turai ya kara tabbatar da cewa tana iya tabuka abin a-zo-a-gani a gasar Club World Cup ta bana da aka sauyawa fasali.

Dortmund za ta yi fatan samun nasara a wasan gaba da za ta fafata da kungiyar Mamelodi Sundowns ta Afirka ta Kudu.

AFP

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • “Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • Dortmund ta yi canjaras da Fluminense a Club World Cup
  • Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu
  • Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga