An bukaci Majalisar Dokoki ta Kasa da ta kafa doka wacce za ta tanadi hukuncin kisa ga masu safarar da kuma masu shan miyagun kwayoyi, domin kare rayuwar ‘yan kasa.

Wannan kiran ya fito ne daga shirin KAKAKI na FRCN Kaduna FM, inda masu kira suka bayyana ra’ayoyinsu a yayin tattaunawa da mai gabatar da shirin.

Masu magana sun nuna damuwa kan illar safarar miyagun kwayoyi a kasar, musamman yadda yake shafar matasa, wadanda ake kallon su a matsayin shugabannin gobe.

Alhaji Gaddafi Rigasa da Hajiya Aisha Mando sun jaddada bukatar hukumomin tsaro su kara zage damtse wajen yaki da wannan matsala, domin inganta ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.

Sai dai sun kuma ba da shawarar a farfado da masana’antu a yankin Arewa a matsayin hanya daya daga cikin hanyoyin rage rashin aikin yi, wanda ke haddasa lalacewar matasa da kuma tabarbarewar tsaro.

SULEIMAN KAURA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwayoyi Safara

এছাড়াও পড়ুন:

Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran

Farashin Man Fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin da Isra’ila ta kai wa Iran, lamarin da ya tayar da hankalin masu zuba jari.

Ana fargabar cewa rikicin da ke ƙara taɓarɓarewa tsakanin ƙasashen biyu zai iya kawo tangarɗa wajen samar da man fetur daga yankin Gabas ta Tsakiya.

An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8

Wani muhimmin wurin da ake safarar man fetur na duniya, wato mashigar Hormuz da ke kusa da Iran na da matuƙar tasiri, domin kashi ɗaya cikin biyar na dukkanin man da ake fitarwa daga nan ne ake bi da shi.

Amma duk da haka, kasuwannin hannun jari sun fuskanci faɗuwar daraja saboda rashin tabbas da harin ya haifar.

Sai dai darajar wasu hajojin da ake ɗauka amintattu a lokutan rikicin irin su zinariya da kuɗin ƙasar Japan, Yen sun tashi sama, domin masu zuba jari na ƙoƙarin neman mafaka a cikinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe