Jiragen Yakin HKI Sun Kai Wa Kudancin Lebanon Hari Da Safiyar Yau Alhamis
Published: 3rd, April 2025 GMT
Rahotanni daga kasar Lebanon sun ce jiragen yakin HKI sun kai hari a garin “Naqura” dake kudancin Lebanon da safiyar yau Alhamis.
Jiragen yakin na ‘yan sahayoniya sun kai harin ne har sau uku ajere akan wata tsohuwar cibiyar kiwon lafiya dake cikin garin, haka nan kuma akan wasu gudajen mutane da suke a kusa.
Ya zuwa yanzu dai babu cikakken bayani akan asarar rayuka sanadiyyar wadannan hare-haren na’yan sahayoniya.
A shekaran jiya Talata ma dai sojojin na mamaya sun kai wa unguwar Dhahiya dake birnin Beirut hari wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama da kuma jikkata wasu.
Hari na shekaran jiya shi ne irinsa na biyu a cikin unguwar Dhahiya tun bayan tsagaita wutar yaki. Haka nan kuma suna ci gaba da kai wasu hare-haren a kudancin Lebanon daga lokaci zuwa lokaci.
Kungiyar Hizbullah ta yi gargadin cewa, ya zama wajibi ga gwamnatin kasar da ta yi amfani da dukkanin hanyoyin da take da su domin takawa ‘yan sahayoniyar birki, gabanin ita ta dauki matakin da ya dace.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.
Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.
Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,