Isra’ila na karbe yankuna a zirin Gaza
Published: 2nd, April 2025 GMT
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa sojojin kasar na karbe iko da wasu yankunan zirin Gaza, a wani mataki na kara matsin lamba kan kungiyar Hamas domin tilasta ta sakin mutanen da ta ke garkuwa da su.
“Muna karbe zirin Gaza tare da kara matsin lamba mataki-mataki domin tilasta su mayar da mutanen da aka yi garkuwa da su,”inji Netanyahu a wani faifan bidiyo da ofishinsa ya fitar.
Ya kara da cewa, Sojoji na karbe yankuna, suna kai farmaki kan ‘yan wadanda ya danganta da ‘yan ta’adda in ji shi, yana mai sanar da samar da wata sabuwar hanya karkashin ikon Isra’ila don raba garuruwan Khan Younis da Rafah (kudu).
Tunda farko dama ministan tsaron Isra’ila Israel Katz ya sanar a Larabar nan cewa, kasarsa ta fadada kaddamar da hare-haren soji a sassan zirin Gaza, yana mai barazanar dakarun Isra’ila za su kwace karin yankuna a zirin da nufin samar da yankuna masu tsaro da za su raba Isra’ila da wurare masu fama da tashin hankali.
Cikin wata sanarwa, mista Katz ya ce matakin fadada ayyukan sojin zai kunshi fadada kwashe mutane daga yankunan da ake dauki ba dadi a Gaza.
Isra’ila dai ta kawo karshen wa’adin tsagaita wuta na watanni 2 tun a ranar 18 ga watan Maris da ya shude, inda ta koma kaddamar da munanan hare-hare ta sama da kasa kan wuraren da Falasdinawa ke fakewa.
A jiya Talata, hukumomin lafiya a Gaza sun ce kawo yanzu sabbin hare-haren sun sabbaba rasuwar Falasdinawa 1,042 tare da jikkata wasu 2,542, yayin da rikicin da ya barke tun daga watan Oktoban shekarar 2023 zuwa yanzu, ya haddasa jimillar asarar rayukan Falasdinawa 50,399, tare da jikkata wasu 114,583.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
Shugaban kungiyar Hamass ya bayyana cewa HKI da gwamnatin kasar Amurka sun janye daga tattaunawa tsakaninsu da kungiyar ne don sake komawa yaki har zuwa lokacinda zasu shafe falasdinawa a gaza.
Tashar talabijin nta Presstv a nan Tehran ya nakalto Kkalilul Hayya, yana fadar haka a wani jawabin da aka watsa a tashoshin talabijin nay au Litinin.
Alhayya ya bayyana cewa akwai ci gaba a tattaunawar tsagaiuta wuta tsakanin kungiyar da HKI da kuma Amurka, amma janyewar HKI da kuma Amurka a wannan tattaunawar wata dasisa ce don ci gaba da kissan kiyashi a gaza.
Ya ce: masu shiga tsakanin sun tabbatar da cewa akwai ci gaba a tattaunawar da ake yi a doha, sai dai sun janye ne don samun lokacinda da zasu gaggauta kissan Falasdinawa a Gaza, don cimma mummunan manufofinsu a gaza.
Dangane da rabon kayakin agaji wanda HKI da Amurska suka shira kuma Alhayya ya yi allawadai da shi ya kuma kara da cewa cibiyoyin bada agajin tarko ne na kara kissan Falasdinawa a Gaza.
Ya kara da cewa shirin GHF na Amurka da kuma HKI shiri ne na kissan karin Falasdinawa bayan sun sanyasu cikin yunwa na kimani watanni biyu kafin su fara rabon abinda suke kira agaji.