Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba
Published: 22nd, March 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta kama mutum 347 da ake zargi da haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba a sassa daban-daban na Najeriya, inda aka gurfanar 143 a kotu.
Kama mutanen ya biyo bayan kafa wata runduna a shekarar 2024 don daƙile ayyukan haƙar ma’adanai ba ƙa’ida ba.
Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDP Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a RibasMinistan Ma’adanai, Dele Alake, ya ce gwamnati na ƙoƙarin tabbatar da an hukunta mutum 327 da ke gaban kotu.
“A wannan watan, Babbar Kotun Tarayya da ke Ilorin ta yanke wa wasu ‘yan kasashen waje guda biyu, Yang Chao da Wu Shan Chuan, hukuncin ɗaurin gidan yari kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba.
“Muna jinjina wa EFCC saboda ƙoƙarinta na gurfanar da masu aikata laifin,” in ji Alake.
Ministan ya ƙara da cewa runduna da aka kafa ta ƙwato wuraren haƙar ma’adanai guda 98, kuma ta gano wasu haramtattun wurare guda 457.
Gwamnati na shirin faɗaɗa ayyukan rundunar zuwa wasu jihohi tare da amfani da fasaha kamar jiragen sama marasa matuƙa da sauran na’urori don sanya ido.
“Rundunar ta ƙwace wuraren da wasu suka mamaye sama da shekaru 10 ba bisa doka ba.
“Wannan zai taimaka wajen bunƙasa kuɗaɗen shiga daga ɓangaren ma’adanai,” in ji shi.
Ministan ya tabbatar da cewa gwamnati za ta ƙara yawan jami’an tsaro da kayan aiki domin daƙile ayyukan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba.
Ya gargaɗi duk masu aikata irin waɗannan laifuka da su daina, ko kuma su fuskanci hukunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Haƙar Ma adanai Karya Doka haƙar ma adanai ba bisa ƙa ida ba
এছাড়াও পড়ুন:
Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza
Mummunar yunwa a Gaza.. Wakilin gidan talabijin na Al-Alam ya bayyana cewa: Shi da iyalansa kwana biyu ba su ci abinci ba
Wakilin gidan talabijin na Al-Alam na kasar Iran ya ruwaito cewa: An samu barkewar yunwa mai tsanani a Gaza, inda ya tabbatar da cewa ya kwashe kwanaki biyu bai ci komai ba.
Basil Khairudden wakilin gidan talabijin na Al-Alam a Gaza, ya ce: “A ranar Juma’a, shi da iyalinsa da daukacin al’ummar Gaza ba su iya samun ko da biredi guda da za su ci ba, sakamakon yunwa da ake fama da ita a Gaza.”
Ya tabbatar da cewa a Gaza akwai mutanen da ba su ci abinci ko da sau daya a tsawon kwanaki uku. A ranar Juma’a mutanen Gaza sun yi ta yawo a kasuwanni, tituna, da unguwanni ba tare da samun kilo guda na gari ba.