Leadership News Hausa:
2025-11-03@07:22:12 GMT

Sin Za Ta Kara Daidaita Matakan Jawo Jarin Waje

Published: 22nd, March 2025 GMT

Sin Za Ta Kara Daidaita Matakan Jawo Jarin Waje

Mai magana da yawun ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin He Yongqian, ta ce kasar za ta aiwatar da matakai na kara daidaita manufar jawo jarin waje a shekarar nan ta 2025, da aiwatar da matakan bude kofa a karin sassa, da kyautata yanayin kasuwanci a fannin.

He Yongqian, wadda ta bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudana a jiya Alhamis, ta ce ya zuwa yanzu kasar Sin ta baiwa wasu kamfanoni masu jarin waje 13 damar shiga hada-hadar inganta hidimomin wayar tarho, yayin da aka kaddamar da ayyuka masu jarin waje sama da 40 a fannin fasahar cin gajiya daga halittu masu rai.

An kuma amince da fara aikin cikakkun asibitoci 3 masu jarin waje.

Jami’ar ta kara da cewa a bana Sin za ta fadada sassan bude kofa a fannin ayyukan gwaji, wanda hakan zai mayar da hankali ga sassa kamar na raya ilimi da al’adu. Bugu da kari, a cewar jami’ar, ma’aikatarta ta taimaka wajen warware wasu batutuwa sama da 500, wadanda suka shafi kamfanoni masu jarin waje ta hanyar hawa teburin shawara, tana mai alkawarta aniyar kasar Sin ta ci gaba da aiki tukuru wajen inganta hidimomi, da yanayin gudanar da hada-hadar kasuwanci ga masu zuba jari na ketare. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: masu jarin waje

এছাড়াও পড়ুন:

Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona da ke Sipaniya na ƙoƙarin ɗauko Victor Osimhen a matsayin wanda zai maye gurbin Robert Lewandowski wanda ke fama da matsalar raunuka

Ɗan jaridar ƙasar Sifaniya, Gabriel Sans na Mundo Deportivo ya bayyana cewar, Barcelona na neman wanda zai maye gurbin Robert Lewandowski a matsayin mai jefa ƙwallo a raga, hakan ne ya sa ƙungiyyar ta amince da ɗaukar Osimhen.

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

A ƙarshen kakar bana ne ake tunanin up Lewandowski zai bar Barca, wanda zai tilasta wa ƙungiyyar neman wani zaƙaƙurin ɗan wasan gaba mai ciyo ƙwallo.

Victor Osimhen dai a bazarar nan ne ya koma Galatasaray bayan barin Napoli ta Italiya.

Osimhen dai ba ya ɓoye aniyarsa ta buga wasa a ɗaya daga cikin manyan gasannin Nahiyyar Turai biyar ba, ciki har da Firimiya ta Ingila da LaLiga ta Sifaniya, inda Barcelona ke cikin manyan ƙungiyoyin gasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa