Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
Published: 22nd, March 2025 GMT
Majalisar wakilai ta tarayya ta yi watsi da zargin da ake yi ga ‘yan majalisar tarayya na cin hanci da rashawa domin marawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu baya na ayyana dokar ta baci a jihar Ribas.
Dan majalisa mai wakiltar mazabar Gwaram daga jihar Jigawa, Honarabul Yusuf Shittu Galambi, ne ya kare majalisar a yayin da ake ta cece-kuce kan batun kafa dokar ta-baci a jihar Ribas, inda wasu kungiyoyi ke zargin majalisar dokokin kasar da yin kasa a gwiwa wajen yanke hukunci.
Sai dai, Galambi a wata sanarwa da ya fitar a yau Asabar, ya ce babu gaskiya a ikirarin na cewa an tursasa ‘yan majalisar kan matakin da shugaban kasar ya dauka.
A cewarsa, yawancin mambobin sun goyi bayan matakin ne saboda ceto dimokuradiyya da kare muradun al’ummar jihar Ribas.
Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa
Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia
Dan majalisar ya bayyana cewa majalisar ta yanke shawarar ne bisa son tabbatar da kishin kasa, hadin kan siyasa, zaman lafiya, da kare dimokuradiyya.
“Na yi mamakin yadda kafafen yada labarai suka rika yada labaran karya, musamman kan zargin da ake yi mana, cewa mun an tilasta mana mu zartar da kudurin goyon bayan matakin da shugaban kasa ya dauka a jihar Ribas da kuma karbar daloli”
“Ya kamata ‘yan Najeriya su yaba da rawar da ‘yan majalisar dokokin kasar ke takawa wajen neman shugaban kasa ya kafa wata tawagar sasanta yan siyasa kafin karewar wa’adin dokar ta-baci na watanni shida.
Ya kuma jaddada cewa dole ne a kare dimokradiyya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fubara dokar ta baci jihar Ribas
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.
Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.
“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.
Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.
Gwamnan ya kuma sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria