INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye
Published: 3rd, April 2025 GMT
Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta bayyana cewa buƙatar da wasu suka shigar don yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Mazaɓar Kogi ta Tsakiya kiranye, bai cika sharuɗa ba.
INEC ta ce yunƙurin bai cika sharuɗan Sashe na 69(a) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanadar ba.
Bello Turji ya kashe manoma 11 a wani sabon hari a Sakkwato NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ‘Ya’yansuWannan sanarwa ta fito ne daga shafukan sada zumunta na INEC a ranar Alhamis, 3 ga watan Afrilu, 2025.
Wasu ƙungiyoyi sun yi ƙoƙarin yi wa Sanata Natasha kiranye, wanda suka ce Sanatan na neman jefa su cikin rikicin da ka iya hana su samun romon dimokuraɗiyya.
Ƙungiyoyin sun miƙa ƙorafinsu ga INEC bisa hujjar cewa ba ta yi musu wakilci mai kyau ba.
Sun yi iƙirarin tattara sama da sa hannun mutum 250,000 daga cikin masu kaƙa ƙuri’a kimanin 480,000 da ke yankin.
Sanata Natasha, ta fuskanci ƙalubale a siyasa a baya-bayan nan, ciki har da dakatarwar tsawon watanni shida d Majalisar Dattawa ta yi mata bisa zargin aikata rashin ɗa’a.
Ta ƙalubalanci wannan hukunci, inda ta bayyana cewa an dakatar da ita ne saboda zargin cin zarafi da ta yi wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.
Wannan batu ya haddasa muhawara mai zafi kan haƙƙin mata da yanayin siyasar Najeriya.
Yadda INEC ta yi watsi da buƙatar tsige ta na nuni da tsauraran sharuɗan da ake buƙata kafin batun kiranye ya samu ƙarbuwa.
Wannan yana jaddada yadda ake buƙatar bin dokoki da tsari kafin a iya aiwatar da yi wa wani ɗan majalisa kiranye.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kiranye Majalisar Dattawa
এছাড়াও পড়ুন:
Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
Bayo Onanuga, Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, ya ce wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu ne kawai saboda ya fito daga Kudancin Najeriya.
Yayin wata hira da Trust Radio, Onanuga ya ce maganar cewa ana yi wa Arewacin Najeriya wariya ba gaskiya ba ce, face tsantsar siyasa kawai.
Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin TarayyaYa ce ƙorafin da Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), ta yi na cewa an yi watsi da Arewa wajen naɗe-naɗen muƙaman gwamnati da ayyukan ci gaba, wata dabara ce kawai don rage ƙimar shugabancin wanda ya fito daga Kudu.
Ya shawarci ’yan siyasar Arewa da su yi haƙuri, kamar yadda ɓangare Kudu ya yi lokacin mulkin marigayi Muhammadu Buhari, wanda ya shugabanci ƙasar har na tsawon shekaru takwas.
“Shugaba Tinubu ɗan Najeriya ne kamar kowa. Ya cancanci yin shekaru takwas a kan mulki kamar yadda Buhari ya yi. Ka da mu lalata ƙasa saboda son zuciya,” in ji Onanuga.
Dangane da zargin cewa an fi bai wa ’yan Kudu muƙamai, Onanuga ya ce masu sukar Tinubu su kawo hujjoji da ƙididdiga maimakon su ci gaba da yin zargin da ba shi da tushe.
Ya ƙara da cewa babu wani yanki da ba shi da matsalar hanyoyi ko ayyukan da ba a kammala gama ba, amma ya ce gwamnatin yanzu na ƙoƙarin gyara abubuwan da ta gada.
“Kafin ku zargi gwamnati, sai ku binciki gaskiyar lamarin. Wannan duk siyasa ce kawai don a raina Shugaban Ƙasa,” in ji shi.
Onanuga, ya kuma kare matakin da Tinubu ke ɗauka wajen inganta tsaro.
Ya ce an samu ci gaba sosai, inda ya kafa misalin cewar dukkanin shugabannin tsaro daga yankin Arewa suka fito.
Ya ce yanzu yana iya yin tafiya daga Kaduna zuwa Abuja cikin kwanciyar hankali, tafiyar da a da ta ke da hatsari sosai.