Aminiya:
2025-06-15@08:35:16 GMT

Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi

Published: 1st, April 2025 GMT

Ana tuhumar wata ma’aikaciyar kamfanin masaka a Jihar Goias ta ƙasar Brazil da laifin saka wa abokan aikinta guba bayan ta yi jayayya da su a kan abin da matar ta kira da rashin adalci wajen ƙarin matsayi da kamfanin ya yi.

Lamarin ya faru ne a wata masana’anta da ke Abadia de Goias, wani gari a yankin Goiânia Metropolitan.

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Za Su Kwaɗaita Muku Azumtar Sitta Shawwal Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari

’Yan sanda sun yi iƙirarin cewa, kyamarar daukar hoto cikin sirri (CCTV) ta kama wadda ake zargin mai shekara 38 tana buɗe wasu gorunan abin sha, wanda daga bisani wata ma’aikaciya ta sha, inda ta ji wani zafi a makogwaronta.

Binciken da aka gudanar ya nuna cewa, an sami wani nau’in ɗanɗano mai ƙarfi a cikin ruwan, wanda ke nuna cewa, wacce ake zargi da laifin tana son zuba wa abokan aikinta guba.

Shaidu sun bayyana cewa, matan biyu abokan juna ne, amma dangantakarsu ta yi tsami bayan ɗaya daga ciki ta samu ƙarin girma, wanda bai yi wa wadda ake zargi da laifin daɗi ba.

Sun yi ta jayayya, wanda ake zargin lamarin ya kai ga matakin zuba gubar.

’Yan sandan yankin sun shaida wa manema labarai cewa, wanda ake zargin mai shekara 38, ta kuma shiga ɓangaren da ake ajiye sinadarai na kamfanin, ba tare da izini ba.

An yi imanin cewa, ta haka ne aka gano ta yi amfanin da sinadaran a matsayin guba.

Bayan ɗaya daga cikin ma’aikatan ta sha, ta gano cewa akwai matsala, inda ta kira motar ɗaukar marasa lafiya, aka garzaya da ita asibiti domin duba ta, amma ta warke sarai, sai dai likitoci sun ce, an yi yunƙurin kashe ta.

‘Yan sanda sun kama wadda ake zargin a ranar 27 ga Fabrairu, bayan sun duba kyamarori na CCTV don gano abin da ake zargin ta, kuma ta amince da gurbata abin shan ga abokan aikinta bayan sun yi wata jayayya.

Mai yiwuwa za a tuhume ta da laifin yunƙurin kisan kai, wanda ke da hukuncin ɗaurin shekar 6 zuwa 20 a gidan yari.

Yadda kyamara ta ɗauki hoton matar tana aika-aikar

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Brazil da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri

A wani bayani na hadin gwiwa da hukumar makamashin Nukiliya ta Iran da kuma ma’aikatar harkokin wajen Iran su ka fitar, sun bayar da umarnin a bude wani wuri na daban na sirri domin ci gaba da tace sanadarin Urani’um, sannan kuma a maye gurbin bututu tace sanadarin mai  mataki na daya, da mai mataki na shida a cibiyar “Pardo.”

Bayanin dai ya zo ne a matsayin mayar da martani ga sanarwar da ta fito daga kwamitin alkalai na hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa akan Iran.

Bugu da kari, bayanin na Iran ya kuma ce; A kodayaushe jamhuriyar musulunci ta Iran tana aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta, kuma har ya zuwa yanzu babu wani rahoto na hukumar wanda ya bayyana cewa; Iran ba ta aiki da ka’idojin hana yaduwar makaman Nukiliya.”

Haka nan kuma bayanin ya ambaci cewa; Tare da cewa Iran tana daukar rahoton da cewa na siyasa ne, wanda Amurka da kasashen turai suke amfani da hukumar a matsayin makami, ba tare da dogaro da wani dalili na ilimi ba.

Har ila yau Iran din ta zargi Amurka da kasashen na turai da wuce gona da iri wajen tsara rahoton da yake cin karo da rahoton da shugaban hukumar ta makamashin Nukiliya ya fitar, wanda bai sami wani abu mai  shiga duhu ba a cikin Shirin na Iran na zama lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato