Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
Published: 29th, March 2025 GMT
Kwamandan sojojin ruwa na dakarun IRGC Rear Admiral Ali-Reza Tangsiri ya tunatar da gwamnatin Amurka kan cewa idan ta aikata wawta ta kaiwa cibiyoyin Nukliyar kasar zata gamu da maida martani mai tsanani.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Tansiri yana fadar haka a kan jirgin ruwa mai daukar jiragen saman yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa a cikin tekun farisa wanda aka sanyawa suna Shahid Baghiri mai kuma tsawon mita 180.
Labarin ya kara da cewa gwamnatin shugaba Donal Trump na kasar Amurka ta bawa Iran razarar watanni biyu ta amince da zauna kan teburin tattaunawa da ita kan shirinta na makamashin nukliya ko kuma ta yi shirin yaki da kasar ta Amurka.
Dakarun na IRGC dai sun gudanar atisai a ranar Qudus ta duniya a cikin tekun na farisa tare da jiragen ruwan yaki manya-manya da kanana wadanda suka kai kimani 3000.
Babban kwamandan ya kammala da cewa babu wani jirgin leken asirin Amurka da ya shigo sararin samaniyar kasar Iran kuma ba zamu taba barin haka ya faru ba. Yace zasu kare kasashen daga duk wanda yake son shigarta ba tare da amincewrasu ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Kai Ziyara Zuwa Kasar Oman don Karfafa Kyakkyawar Alakar Kasashen Biyu
Kafin tashinsa zuwa kasar Oman shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Suna neman kyakkyawar dangantaka da maƙwabtansu
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya tabbatar kafin ya tashi daga filin tashi da saukar jiragen sama na birnin Tehran zuwa birnin Muscat a yammacin yau Talata cewa: Makasudin ziyarar tasa zuwa kasar Oman ita ce kulla kyakkyawar alaka da kasashe makwabta, kuma alaka tsakaninsu tana bunkasa kowace rana.
Shugaba Pezeshkian da yake zantawa da manema labarai a filin tashi da saukar jiragen sama na Mehrabad ya bayyana cewa: A halin yanzu yawan ciniki tsakanin Iran da Oman ya kai dalar Amurka biliyan 2.3, yana mai jaddada bukatar ci gaba da karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.
Shugaba Pezeshkian ya ce: Zai gudanar da wannan ziyara ce bisa gayyatar da Sultan Haitham bin Tariq Al Said ya yi masa a hukumance, kuma bisa ga dukkanin manufofin gwamnati da Jagoran juyin juya halin Musulunci, manufar wannan ziyara ita ce kulla alaka mai zurfi da kyakykyawan dangantaka da kasashen makwabta ciki har da masarautar Oman, haka kuma an shirya fadada dangantakar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a dukkanin bangarori na siyasa da tattalin arziki da zamantakewa.