Leadership News Hausa:
2025-11-02@06:08:51 GMT

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

Published: 29th, March 2025 GMT

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

Wannan hanya, na matukar taimakawa sosai wajen sarrafa sinadarin insulin a jikin mutum.

 

2-Maganin Hawan Jini (Hypertension)

Ganyen mangwaro na rage matsin jini, sannan kuma yana karfafa jijiyoyin jini.

Saboda haka, a nan sai a nemi sabbin ganyen mangwaro, a tafasa su sosai a tace, sannan a sha rabin kofi da safe da kuma yamma.

 

3-Maganin Basir Sadidan

Idan ana fama da basir, za a iya amfani da ganyen mangwaro don rage kumburi da ciwo.

Bayan an samu wannan ganye na mangwaro, sai a busar da shi a kuma daka shi har sai ya zama gari. kana sai a dauki cokali daya na garin a hada da rabin kofi na ruwan dumi, sannan a zuba zuma a ciki kadan a sha kullum har sai an samu sauki.

 

4-Maganin Cututtukan da ke Cikin Baki

Idan ana fama da kuraje a baki, zubar jini daga hakora ko kuraje a harshe, ganyen mangoro na da matukar amfani wajen magance su.

A nan, tafasa ganyen za a yi a tace, sannan a yi amfani da ruwan wajen wanke baki sau uku a rana. Idan ana so kuma za a iya kara gishiri dan kadan, don karin karfi.

 

5-Maganin kunar Wuta

Idan aka samu kuna, ganyen mangoro na taimakawa wajen rage radadi da saurin warkewa.

Saboda haka, sai a busar da ganyen, a kone shi har sai ya zama toka. Sai a yi amfani da tokar wajen shafawa a wurin da aka konen.

 

6-Maganin Cututtukan da Suka Shafi Ciki

Ganyen mangwaro na taimakawa wajen magance matsalolin ciki, kamar ciwon ciki da kuma gudawa.

A nan za a tafasa ganyen ne, sannan a rika shan ruwan kullum sannu a hankali.

 

7-Rage Zafin Jiki da Rashin Nutsuwa (Stress & Andiety)

Idan ana fama da zafin jiki ko rashin hutu, ganyen mangwaro na taimakawa kwarai da gaske wajen kawar da su.

Za a tafasa shi, sannan a rika shan ruwan ko kuma a rika yin wanka da shi, domin samun nutsuwa.

8-Maganin Cututtukan Huhu (Tari, Mura da Sanyi)

Ganyen mangwaro na taimakawa wajen maganin tari, mura da kuma sanyi.

Ana tafasa shi a sha ruwan, domin rage tari da samun waraka daga cutar mura da kuma ta sanyi.

 

9-Inganta Lafiyar Mahaifa da Haihuwa

Ganyen mangwaro na da matukar amfani ga mata masu fama da matsalolin mahaifa.

Har ila yau, yana taimakawa wajen tsaftace mahaifa da kuma kara samun damar haihuwa.

don haka, a nan sai a tafasa ganyen a tace shi, sannan a rika shan sa da dumi.

 

10-Maganin Makakin Makogwaro da Ciwon Wuya

Idan ana fama da kuraje a makogwaro ko ciwon wuya ko kuma makaki, ganyen mangwaro na taimakawa kwarai da gaske wajen warkar da su.

Saboda haka, sai a tafasa shi sosai a yi amfani da ruwan ta hanyar kurkurawa da safe da kuma yamma.

 

Bugu da kari, ganyen mangwaro na da matukar amfani ga lafiyar jikin dan’adam. Idan ana son cin gajiyar fa’idarsa yadda ya kamata, yana da kyau a rika amfani da shi akai-akai.

Sannan, duk da haka; yana da matukar kyau a nemi shawarar likita kafin

a fara amfani da kowane irin maganin gargajiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Mangwaro Sirri ganyen mangwaro na taimakawa Ganyen mangwaro na taimakawa na taimakawa wajen na da matukar

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini

Shugaban kasar Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya fada wa Shugaban Amurka Donald Trump cewa; a Nigeria ba a lamunta da duk wani rikicin addini.

Shugaban na kasar Najeriya ta mayar wa da Tinubu martani ne saboda yadda ya bayyana Najeriya a matsayin kasa mai jawo damuwa ta musamman”, bisa zargin cewa Mabiya addinin kiristanci suna fuskantar barazanar karewa, ya kuma yi alkawalin cewa Amurkan za ta ba su kariya.

Donald Trump ya ce; Kiristoci suna fuskantar barazanar karar da su a Nigeria, an kuma kashe dubban kiristoci a kasar.”

A yau Asabar, kwana daya daga wancan zancen na Tinibu ne dai shugaban kasar ta Nigeria Bola Ahamd Tinubu mayar da martanin da ya kunshi cewa:  Nageria kasa ce ta Demokradiyya, kuma tsarin mulkinta ya lamuncewa kowa ‘yancin yin addini.”

Har ila yau shugaban kasar ta Najeriya ya ce; Tun daga 2023 gwamnatinmu take mu’amala da hulda da dukkanin malaman kirista da musulmi, kuma tana ci gaba da magance matsalar tsaro da ta shafi dukkanin mutanen kasar daga kowane addini a cikin yankunan kasar.

Shugaba Tinubu ya kuma ce; Bayyana Nigeria a matsayin kasa wacce ake fada da addini, ba ya nuni da hakikanin yadda rayuwa take a kasar, kuma ba a yi la’akari da yadda gwamnati take aiki tukuru domin kare ‘yancin yin addini da akidun mutanen Nigeria ba.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna