Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar
Published: 3rd, June 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta
Wata sabuwar tashin-tashina ta sake kunno kai a yankin kahon Afirka a daidai lokacin da shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya yi gargadi kai tsaye ga firaministan Habasha Abiy Ahmed, inda ya yi kashedin sake kaddamar da wani yaki.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasar Habasha ke kokarin shiga bangaren ruwa Eritra da kuma tabarbarewar dangantakar bangarorin biyu tun bayan rikicin Tigray.
A cikin wani jawabi da ya yi ta gidan telebijin, shugaba Afwerki ya yi gargadin cewa adadin yawan jama’ar Habasha ba zai tabbatar da nasarar soji ba, yana mai nuni da dabarun yakin da Habasha ta yi amfani da su a yakin da ya gabata, yana mai cewa duk da yawan sojojinta amma bata samu nasara ba.
Afwerki ya kira matakin na Abiy a matsayin “rashin hankali” tare da danganta hakan da matsalolin siyasar cikin gidan Habasha. Ya kuma nanata cewa Eritrea ba za ta amince da keta hurumin kasarta ba, ya kuma bukaci Habasha da ta warware matsalolin cikin gida kafin ta yi la’akari da daukar mataki a kan waje.
Kasar Habasha wadda ita ce kasa mafi yawan al’umma a gabashin nahiyar Afirka, ta dade tana neman shiga Tekun Bahar Maliya, ayyin da Eritiriya take yin matukar kaffa-kaffa da wannan manufa ta Habasha.
Kasashen Eritrea da Habasha sun jima suna zaman doya da manja tun bayan da Eritrea ta kwashe shekaru 30 tana yakin neman ‘yencin kai da mulkin Habasha, wanda ya kai ga samun ‘yancin kai a 1993.
Rikicin da ya fi kamari ya faru ne daga 1998 zuwa 2000, lokacin da wani mummunan yakin kan iyaka ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 100,000. Duk da yarjejeniyar zaman lafiya da aka sanya hannu a kanta a cikin 2018, amma babu wani tabbaci kan ci gaba da wanzuwar wannan yarjejeniya.
Habasha tana da yawan jama’a miliyan 130, Eritrea miliyan 3.5 kawai.