Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa
Published: 3rd, June 2025 GMT
Bidiyon ya jawo martani daban-daban a tsakanin jama’a.
Wasu sun goyi bayan matakin malamin, inda suka bayyana cewa yana da ‘yancin kare kansa a irin wannan lokaci na rashin tsaro.
Amma wasu sun soki abin da ya yi, inda suka ce zuwa da makami wajen taron jama’a ko addini hatsari ne mai girman gaske.
Daga kanmu, magana ta ƙare.
কীওয়ার্ড: Sakkwato Sheikh Bello Yabo Tsaro Wa azi
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya gana da shugaban kasar Masar a birnin Alkahira
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya gana da shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi a yau Litinin.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arakchi ya isa birnin Alkahira da yammacin jiya Lahadi domin tattaunawa da manyan jami’an kasar Masar.
A yayin wannan ziyara, Araqchi ya gana da ministan harkokin wajen Masar Badr Abdel Aty da shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi inda suka tattauna batutuwan baya-bayan nan a dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da ci gaban yankin, musamman batun kalubalantar laifukan haramtacciyar kasar Isra’ila, da kuma wasu batutuwan kasa da kasa.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya sanar da Shirin ministan harkokin wajen Iran na ziyartar ministan harkokin wajen kasar Masar da Lebanon a wani taron manema labarai da ya kira a yammacin ranar Asabar.