Majalisar Dinkin Duniya da Tarayyar Turai sun ce, tsagaita bude wuta nan take a Gaza ya zama dole.

Da yake magana a wani taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, mataimakin babban sakataren majalisar kan  harkokin siyasa Khaled Khari, ya ba da rahoto game da tabarbarewar al’amura a Gaza bayan da Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da musayar fursunoni da aka kwashe kusan watanni biyu ana aiki da ita.

“A kowace rana, muna kara nisa daga manufar mayar da sauran mutanen da aka yi garkuwa da su zuwa gidajensu lami lafiya,” in ji Khari, yayin da yake magana kan fursunonin Isra’ila da aka yi garkuwa da su a Gaza.

Babban jami’in kula da harkokin siyasa na Majalisar Dinkin Duniya ya yi kira da a dawo da tattaunawar tsagaita bude wuta da kuma kai kayan agaji a Gaza ba tare da wata tangarda ba.

Ya yi ishara da jawabin da babban jami’in agaji na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher ya yi wa UNSC a farkon wannan makon, inda yace yin aiki da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ita ce hanya mafi dacewa domin kare fararen hula  a Gaza, da kuma sako wadanda aka yi garkuwa da su, gami da shigar da kayan agaji da kayayyakin bukatar rayuwa zuwa Gaza.

Khari ya ce jami’an MDD shida na daga cikin daruruwan mutanen da aka kashe tun bayan da Isra’ila ta sake dawo da kai hare-hare a ranar Talata.

A daya bangaren kuma Majalisar Tarayyar Turai ta yi Allah wadai da “rugujewar yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza, wanda ya yi sanadin mutuwa da  jikkatar fararen hula masu yawa a hare-haren jiragen saman Isra’ila a baya-bayan nan”.

Har ila yau, ta bukaci komawa ga aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta nan take, tare da jaddada wajabcin ci gaba zuwa mataki na biyu na yarjejeniyar wanda Isra’ila ta yi fatali da shi.

Majalisar EU ta ce aiwatar da yarjejeniyar na da matukar muhimmanci wajen ganin an sako dukkan wadanda ake tsare da su a Gaza da kuma gidajen kurkukun Isra’ila, tare da cimma nasarar kawo karshen fada na dindindin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita bude wuta Majalisar Dinkin Duniya da Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan

Dubban mutane ne suka fito kan tituna a birnin Tel Aviv na Isra’ila ranar Asabar, domin yin kira da a kawo ƙarshen yaƙin Gaza, kwana guda bayan da gwamnatin Isra’ila ta lashi takobin faɗaɗa rikicin tare da ƙwace birnin Gaza.

Masu zanga-zangar da ke riƙe da hotunan waɗanda har yanzu ake garkuwa da su a yankin Falasdinawa sun yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da sakin su ’yan uwansu.

Al-Hilal ta ɗauki Nunez daga Liverpool ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki

’Yan jaridar AFP a wajen gangamin sun ƙiyasta adadin waɗanda suka halarci taron a matsayin dubbai, yayin da wata ƙungiya da ke wakiltar iyalan wadanda aka yi garkuwa da su ta ce mutane kusan 100,000 ne suka yi dafifi.

Hukumomin ƙasar ba su bada wasu alƙaluma mutane da suka shiga zanga-zangar ba, amma sun hakikance lalai ya, zarta duk wasu gangamin da aka yi a baya na adawa da yakin.

Masu zanga-zangar sun ƙarkare da aike wa Firaminista Benjamin Netanyahu saƙo da kakkausar murya.

Shahar Mor Zahiro, ɗaya daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da ɗan uwansa, ya shaida wa AFP cewar: “Idan ka mamaye sauran sassan Gaza kuma aka kashe sauran ’yan uwanmu da ake garkuwa da su, za mu bi ka har cikin harabar dandalin Square, ko a lokacin yakin neman zaɓe ko a kowane lokaci ko waje.”

A ranar Juma’ar da ta gabata, majalisar ministocin tsaron Netanyahu ta amince da gagarumin farmaki na kwace birnin Gaza, lamarin da ya janyo cece-kuce da tofin Allah tsine daga cikin gida da ƙasashen duniya.

Wasu ƙasashen ketare, ciki har da wasu kawayen Isra’ila, sun yi ta matsa kaimi don ganin an tsagaita wuta domin tabbatar da dawowar wadanda aka yi garkuwa da su da kuma taimakawa wajen rage matsalar jin kai a yankin.

Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasɗinu a Istanbul

Dubban masu zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu sun taru a Dandalin Beyazit na Istanbul a ranar Asabar bayan sallar Magariba, domin nuna adawarsu ga kisan kiyashi da ƙaƙaba yunwa da Isra’ila ke yi a Gaza.

Gangamin, wanda ya haɗa da ƙungiyoyin ba da gwamnati da kuma jama’a da dama, ya ci gaba da tafiya zuwa Masallaci mai tarihi na Ayasofya.

Mahalarta sun yi ƙoƙarin jan hankalin duniya game da matsalar jin kai da ke faruwa a Gaza, tare da nuna goyon baya gare su, yayin da tashin hankali da ƙarancin abinci da magunguna ke ƙara ta’azzara.

Masu shirya zanga-zangar sun yi kira ga al’ummar duniya da su ɗauki matakan gaggawa don kawo ƙarshen wahalhalun.

Isra’ila Na Fuskantar Matsin Lamba Daga Duniya

Isra’ila na fuskantar ƙarin fushin duniya saboda kisan kiyashi da take yi a Gaza, inda ta kashe fiye da mutane 61,000 tun watan Oktoba 2023.

Haren-haren da soja ke kaiwa sun lalata yankin sosai kuma sun haifar da mutuwa ta hanyar yunwa da ƙunci.

A watan Nuwamba da ya gabata, Kotun Hukunta Laifukan Yaƙi ta Duniya ta bayar da sammacin kama Firayiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon Ministan Tsaronsa Yoav Gallant saboda laifukan yaƙi da laifukan cin zarafin ɗan adam a Gaza.

Haka kuma, Isra’ila tana fuskantar shari’ar kisan kiyashi a Kotun Duniya saboda yaƙin da take yi a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza
  • Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza
  • MDD za ta yi zaman gaggawa kan yunƙurin ƙwace Gaza
  • Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan
  • Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10
  • Jamus ta dakatar da ba wa Isra’ila kayayyakin aikin soji saboda shirinta na mamaye Gaza
  • Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno
  • Australia ta gargadi Isra’ila game yunkurin mamaye birnin Gaza
  • Axios: Majalisar ministocin Isra’ila ta amince da sabon shiri na mamaye birnin Gaza
  • Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokokin Yawon Buɗe Ido da Zartar da Shari’a