Aminiya:
2025-05-21@21:54:58 GMT

’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista

Published: 18th, April 2025 GMT

Ministan Wutar Lantarki, Adedayo Adelabu ya bayyana cewa kimanin ’yan Najeriya miliyan 150 ne yanzu ke samun isasshiyar wutar lantarki, yayin da miliyan 80 ke da ƙarancin wutar lantarki.

Ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a yayin taron sabunta sassan ministoci na 2025 da aka gudanar a Abuja, inda ya yi magana tare da ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Malagi, da sauran masu ruwa da tsaki.

ISWAP sun ruguza gadar Mandafuma a Borno ’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a Kaduna

Adelabu ya bayyana cewa ci gaban ya samo asali ne daga shigar Najeriya cikin shirin “Mission 300” – wani gagarumin ƙoƙarin haɗin gwiwa na Bankin Duniya da Bankin Raya Afirka (AfDB) da nufin samar da wutar lantarki ga ‘yan Afirka miliyan 300 nan da shekarar 2030.

“Ƙa’idar ta tsara kyawawan manufofi don haɓaka hanyoyin samar da wutar lantarki, ƙara haɓaka makamashi da inganta hanyoyin magance matsalolin dafa abinci mai tsabta ga miliyoyin ‘yan Najeriya – wato Mission 300, kuma muna samun ci gaba mai kyau a kan wannan,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, “Ina mai farin cikin gaya muku cewa cikin ‘yan Afirka miliyan 300 da Bankin Duniya da AfDB ke son cimmawa, Najeriya na kan hanyar da za ta biya ƙasa da kashi 25 cikin 100, wanda ke nufin kusan ‘yan Najeriya miliyan 75. Da muka gabatar da yarjejeniyarmu, sun amince da mu.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya Adedayo Adelabu Wutar Lantarki wutar lantarki yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta bayyana cewa ta yi jigilar maniyyatan Najeriya 32,549 zuwa Saudiyya don gudanar da Hajjin shekarar 2025.

Wannan adadi ya kai kashi 79.1 na jimillar waɗanda ake sa ran za su yi Hajji daga Najeriya.

DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu” Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba

Mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta ce an kammala jigilar ne ta hanyar amfani da jirage 79 tun daga ranar 9 ga watan Mayu, 2025.

Rahoton Aminiya ya nuna cewa kimanin maniyyata 42,000 ne ake sa ran za su halarci Hajjin bana daga Najeriya.

Jihohi da dama kamar Adamawa da Filato sun kammala jigilar maniyyatansu baki ɗaya.

Jihohin Jigawa da Babban Birnin Tarayya, ana sa ran za su kammala jigilar nasu maniyyatan a yau.

Jihar Kwara, wadda ke da sauran maniyyata 137, za ta kammala kwashe su a a wani jirgi a Jihar Kano da yammacin yau.

Mahajjata daga Jihar Binuwai da yankin Kudu maso Kudu za su tashu tare a jirgi ɗaya da aka tanada da zai tashi a ranar 23 ga watan Mayu, wanda shi ne jirgi na ƙarshe daga yankin.

NAHCON, ta bayyana cewa ba a samu jirgi ko ɗaya da aka soke tashin ba tun da aka fara jigilar.

Sai dai an samu jinkirin tashin wasu jirage da gangan saboda bai wa otel-otel a Madina damar tsaftace ɗakunansu.

Wannan al’amari yana daga cikin tsare-tsaren gudanar da aikin Hajjin bana, musamman idan yawan mahajjatan ya ƙaru a lokaci ɗaya.

NAHCON, ta gode wa mahajjata da ɗaukacin al’ummar Najeriya bisa haƙuri, addu’o’i da goyon baya, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da ƙoƙarin ganin an gudanar da aikin Hajjin cikin tsari da sauƙi ga kowa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
  • Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano
  • Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON
  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • Jihar Jigawa Za Ta Sayi Motoci 36 Ga Mambobin Kungiyar NURTW
  • An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za Ku Kula Da Lafiyar Jikinku
  • Iran Ta Ce Gabatar Da Bukatar Dakatar Da Tashe Makamashin Uranium Karshen Tattaunawar Da Amurka
  • Iyalan Sarkin Da Aka Kama Suna Neman Taimakon Kudin Fanso Shi Miliyan ₦50
  • NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?