Farfesa Bello ya ce gwamnatin jihar ta dage wajen bai wa ’yan mata masu tasowa ingantaccen ilimi da tallafa musu domin su zama masu amfani ga iyalansu da al’ummominsu.

 

Ya bayyana godiyarsa matuka bisa gudunmuwar da Bankin Duniya ke bayarwa, yana bayyana aikin AGILE a matsayin wani gagarumin sauyi wajen canja ra’ayin al’umma game da ilimin ’ya’ya mata.

 

“Kalma ba za ta isa ta bayyana yadda muke jin wannan taimako daga Bankin Duniya ba, musamman game da aikin AGILE. Kungiyar aikin a jihar, karkashin jagorancin Maryam Sani Dangaji, ta yi kokari sosai wajen fadakar da iyaye cewa AGILE yana kokarin taimaka wa yarinya ta gane cikakken kwarewarta,” in ji shi.

 

Farfesa Bello ya kara da cewa gwamnatin jihar ta kuma kaddamar da wani sabon shiri mai suna “Reaching Out to Out-of-School Children” domin rage adadin yaran da ke waje da makaranta a fadin jihar.

 

Haka kuma ya bayyana cewa gwamnati ta ware dala miliyan goma sha shida ($16m) domin gina makaranta a ko wace tazarar kilomita daya a yankunan karkara domin karfafa shiga makaranta.

 

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Yankin na Bankin Duniya, Ousmane Diagana, ya jinjinawa gwamnatin jihar Kaduna kan yadda take jajircewa wajen ganin aikin AGILE ya samu nasara.

 

Diagana ya jaddada muhimmancin ilmantar da ’yan mata, yana rokon dukkan masu ruwa da tsaki da su ci gaba da jajircewa duk da kalubale.

“Idan yarinya ta samu ilimi, gaba dayan al’umma ke amfana,” in ji shi, yana mai jaddada bukatar kawar da duk wani cikas da zai hana ‘yan mata cimma burinsu.

 

Aikin AGILE, wanda Bankin Duniya ke tallafawa, ya zuwa yanzu ya gyara makarantu 665, ya horas da malamai, tare da wayar da kan ‘yan mata game da sauyin yanayi da daukar matakin kare muhalli.

 

Da take zantawa da Radio Nigeria Kaduna, Daraktar Yanki da ke kula da kasashen Yammaci da Gabashin Afirka kan harkokin Ilimi, Lafiya, Kariya ta Zamani da Jinsin Mata, Trina Haque, ta ce Bankin Duniya na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da cewa dukkan ’yan mata masu tasowa sun samu ingantaccen ilimi karkashin aikin AGILE.

Ta kara da cewa Bankin Duniya na aiki kafada da kafada da gwamnonin jihohi da kwamishinonin ilimi domin cimma burin aikin.

 

Ita ma, Jami’ar Kula da Bin Diddigi na aikin AGILE a Kaduna, Yabai Ayis, ta bayyana nasarorin da aka samu a cikin shekaru hudu da suka gabata.

 

“AGILE ya gyara makarantu 550 tare da sake farfado da wasu makarantu 115, wanda ya kai jimillar makarantu 665 da suka amfana daga gyare-gyare daban-daban. Haka kuma, an horas da malamai domin inganta koyarwa a duk makarantu na gwamnati a Jihar Kaduna,” in ji Ayis.

Daya daga cikin wadanda suka amfana da aikin, Success Eliminian, ta yaba wa AGILE bisa sauya dabi’u da al’adun al’umma tare da bunkasa ilimin ’yan mata.

“Aikin AGILE yana sauya tunanin al’umma da al’adunmu. Ya shafe mu ta hanyar ba mu ilmi da da yadda zamu kulada kanmu akan kowane irin kalubale,” In ji ta.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ya ya AGILE Gwamnatin Duniya Hanyar Rayuwar Sauya Bankin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027.

Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta.

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo

“Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna cewa ba sa son a samu hamayya a lokacin zaɓe,” in ji shi.

Galadima ya kuma yi gargadi kan shirin nada wani da ya kira mai lam’a a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin rudani.

“Ina fatan ba gaskiya ba ne, domin idan wannan mutumin ya zama shugaban INEC, ka tabbata cewa wannan gwamnati na neman tayar da yaƙin basasa,” in ji shi.

Sai dai bai ambaci sunan mutumin ba.

Dangane da batun fara yaƙin neman zaɓe da wuri da wasu jam’iyyu ke yi, Buba Galadima ya zargi INEC da gazawa wajen aiwatar da tanade-tanaden dokokin zaɓe.

“Wannan batun fara yaƙin neman zaɓe kafin INEC ta ba da izini, gwamnatin da ke kan mulki ce ta fara shi. Wannan yana nuna cewa INEC ba za ta iya zama mai adalci a irin wannan yanayin siyasa da muke ciki ba,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Alhazai Ta Jigawa Za Ta Shirya Taron Bita Na Musamman Ga Jami’anta
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • Gwamnatin Gombe ta gyara hanyoyin kiwo domin daƙile rikicin manoma da makiyaya
  • Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima