AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
Published: 17th, April 2025 GMT
Farfesa Bello ya ce gwamnatin jihar ta dage wajen bai wa ’yan mata masu tasowa ingantaccen ilimi da tallafa musu domin su zama masu amfani ga iyalansu da al’ummominsu.
Ya bayyana godiyarsa matuka bisa gudunmuwar da Bankin Duniya ke bayarwa, yana bayyana aikin AGILE a matsayin wani gagarumin sauyi wajen canja ra’ayin al’umma game da ilimin ’ya’ya mata.
“Kalma ba za ta isa ta bayyana yadda muke jin wannan taimako daga Bankin Duniya ba, musamman game da aikin AGILE. Kungiyar aikin a jihar, karkashin jagorancin Maryam Sani Dangaji, ta yi kokari sosai wajen fadakar da iyaye cewa AGILE yana kokarin taimaka wa yarinya ta gane cikakken kwarewarta,” in ji shi.
Farfesa Bello ya kara da cewa gwamnatin jihar ta kuma kaddamar da wani sabon shiri mai suna “Reaching Out to Out-of-School Children” domin rage adadin yaran da ke waje da makaranta a fadin jihar.
Haka kuma ya bayyana cewa gwamnati ta ware dala miliyan goma sha shida ($16m) domin gina makaranta a ko wace tazarar kilomita daya a yankunan karkara domin karfafa shiga makaranta.
A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Yankin na Bankin Duniya, Ousmane Diagana, ya jinjinawa gwamnatin jihar Kaduna kan yadda take jajircewa wajen ganin aikin AGILE ya samu nasara.
Diagana ya jaddada muhimmancin ilmantar da ’yan mata, yana rokon dukkan masu ruwa da tsaki da su ci gaba da jajircewa duk da kalubale.
“Idan yarinya ta samu ilimi, gaba dayan al’umma ke amfana,” in ji shi, yana mai jaddada bukatar kawar da duk wani cikas da zai hana ‘yan mata cimma burinsu.
Aikin AGILE, wanda Bankin Duniya ke tallafawa, ya zuwa yanzu ya gyara makarantu 665, ya horas da malamai, tare da wayar da kan ‘yan mata game da sauyin yanayi da daukar matakin kare muhalli.
Da take zantawa da Radio Nigeria Kaduna, Daraktar Yanki da ke kula da kasashen Yammaci da Gabashin Afirka kan harkokin Ilimi, Lafiya, Kariya ta Zamani da Jinsin Mata, Trina Haque, ta ce Bankin Duniya na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da cewa dukkan ’yan mata masu tasowa sun samu ingantaccen ilimi karkashin aikin AGILE.
Ta kara da cewa Bankin Duniya na aiki kafada da kafada da gwamnonin jihohi da kwamishinonin ilimi domin cimma burin aikin.
Ita ma, Jami’ar Kula da Bin Diddigi na aikin AGILE a Kaduna, Yabai Ayis, ta bayyana nasarorin da aka samu a cikin shekaru hudu da suka gabata.
“AGILE ya gyara makarantu 550 tare da sake farfado da wasu makarantu 115, wanda ya kai jimillar makarantu 665 da suka amfana daga gyare-gyare daban-daban. Haka kuma, an horas da malamai domin inganta koyarwa a duk makarantu na gwamnati a Jihar Kaduna,” in ji Ayis.
Daya daga cikin wadanda suka amfana da aikin, Success Eliminian, ta yaba wa AGILE bisa sauya dabi’u da al’adun al’umma tare da bunkasa ilimin ’yan mata.
“Aikin AGILE yana sauya tunanin al’umma da al’adunmu. Ya shafe mu ta hanyar ba mu ilmi da da yadda zamu kulada kanmu akan kowane irin kalubale,” In ji ta.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ya ya AGILE Gwamnatin Duniya Hanyar Rayuwar Sauya Bankin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Buɗe cibiyar horas da sabbin sojoji a Kudu zai taimaka — Janar Shaibu
Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Shaibu ya yaba, ya bayyana cewa buɗe cibiyoyin horas da sabbin kuratan sojoji (Depot) a jihohin Kudu zai ƙara ƙarfin rundunar wajen karɓar sabbin ma’aikata a faɗin ƙasa.
Laftanar-Janar Shaibu ya bayyana cewa za a buɗe sabbin cibiyoyin horas da sabbin kuratan sojojin ne a Osogbo da ke Jihar Osun da kuma Abakaliki a Jihar Ebonyi.
Ya bayyana haka ne a yayin bikin yaye sabbin dakarun soji 3,439 da aka yi a Cibiyar Horas da Sabbin Kuratan sojoji (Depot) da ke Zariya, inda ya shawarce su da su zama masu kishin ƙasa da jajircewa.
Ya yaba wa sabbin sojojin bisa jajircewa, juriya da ƙwarewa da suka nuna a tsawon watannin da suka shafe suna karɓar horo a cibiyar.
Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — TurakiLaftanar-Janar Shaibu ya bayyana ranar a matsayin ranar nuni da babban ci gaba wajen cika manufar rundunar sojojin Najeriya ta faɗaɗa karfin ma’aikata.
Ya taya sabbin sojojin murnar kammala horon farko na soja, wanda, a cewarsa, shi ne matakin farko na doguwar tafiyar sadaukarwa, kishin ƙasa, da hidima ga al’umma.
“Kuna shiga rundunar soja ne a wani lokaci mai muhimmanci a tarihin ƙasarmu, lokacin da ƙalubalen tsaro ya yi yawa. Ku ɗauki wannan dama da muhimmanci domin ku zama wani ɓangare na mafita ga matsalolin ta’addanci da rashin tsaro,” in ji shi.
Ya buƙace su da su riƙe gaskiya, ladabi, da bin ƙa’ida a duk inda suka samu kansu, yana mai cewa horon da suka samu (a Depot NA) ya shirya su wajen fuskantar manyan ayyukan soja na zamani.
Janar Shaibu ya bayyana cewa manufar sauya tsarin rundunar soja a ƙarƙashin jagorancin Babban Hafsan Sojoji na nufin kafa runduna mai ƙwarewa, ɗorewa, da shirye-shiryen fuskantar ƙalubale cikin haɗin kai da sauran hukumomin tsaro.
Ya kuma jinjina wa Kwamandan Depot na Zariya, Janar Ahmadu Bello Muhammad, da malamai da jami’an horo saboda jajircewarsu wajen ganin an kammala horon cikin nasara.
Haka kuma, Babban Hafsan Sojoji ya gode wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu, wanda shi ne Kwamandan Rundunar Sojojin Najeriya, bisa jagoranci da goyon bayan da yake bai wa rundunar, tare da godewa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, da Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli, da al’ummar Zariya saboda kyakkyawar alaƙa da rundunar soja.