Farfesa Bello ya ce gwamnatin jihar ta dage wajen bai wa ’yan mata masu tasowa ingantaccen ilimi da tallafa musu domin su zama masu amfani ga iyalansu da al’ummominsu.

 

Ya bayyana godiyarsa matuka bisa gudunmuwar da Bankin Duniya ke bayarwa, yana bayyana aikin AGILE a matsayin wani gagarumin sauyi wajen canja ra’ayin al’umma game da ilimin ’ya’ya mata.

 

“Kalma ba za ta isa ta bayyana yadda muke jin wannan taimako daga Bankin Duniya ba, musamman game da aikin AGILE. Kungiyar aikin a jihar, karkashin jagorancin Maryam Sani Dangaji, ta yi kokari sosai wajen fadakar da iyaye cewa AGILE yana kokarin taimaka wa yarinya ta gane cikakken kwarewarta,” in ji shi.

 

Farfesa Bello ya kara da cewa gwamnatin jihar ta kuma kaddamar da wani sabon shiri mai suna “Reaching Out to Out-of-School Children” domin rage adadin yaran da ke waje da makaranta a fadin jihar.

 

Haka kuma ya bayyana cewa gwamnati ta ware dala miliyan goma sha shida ($16m) domin gina makaranta a ko wace tazarar kilomita daya a yankunan karkara domin karfafa shiga makaranta.

 

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Yankin na Bankin Duniya, Ousmane Diagana, ya jinjinawa gwamnatin jihar Kaduna kan yadda take jajircewa wajen ganin aikin AGILE ya samu nasara.

 

Diagana ya jaddada muhimmancin ilmantar da ’yan mata, yana rokon dukkan masu ruwa da tsaki da su ci gaba da jajircewa duk da kalubale.

“Idan yarinya ta samu ilimi, gaba dayan al’umma ke amfana,” in ji shi, yana mai jaddada bukatar kawar da duk wani cikas da zai hana ‘yan mata cimma burinsu.

 

Aikin AGILE, wanda Bankin Duniya ke tallafawa, ya zuwa yanzu ya gyara makarantu 665, ya horas da malamai, tare da wayar da kan ‘yan mata game da sauyin yanayi da daukar matakin kare muhalli.

 

Da take zantawa da Radio Nigeria Kaduna, Daraktar Yanki da ke kula da kasashen Yammaci da Gabashin Afirka kan harkokin Ilimi, Lafiya, Kariya ta Zamani da Jinsin Mata, Trina Haque, ta ce Bankin Duniya na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da cewa dukkan ’yan mata masu tasowa sun samu ingantaccen ilimi karkashin aikin AGILE.

Ta kara da cewa Bankin Duniya na aiki kafada da kafada da gwamnonin jihohi da kwamishinonin ilimi domin cimma burin aikin.

 

Ita ma, Jami’ar Kula da Bin Diddigi na aikin AGILE a Kaduna, Yabai Ayis, ta bayyana nasarorin da aka samu a cikin shekaru hudu da suka gabata.

 

“AGILE ya gyara makarantu 550 tare da sake farfado da wasu makarantu 115, wanda ya kai jimillar makarantu 665 da suka amfana daga gyare-gyare daban-daban. Haka kuma, an horas da malamai domin inganta koyarwa a duk makarantu na gwamnati a Jihar Kaduna,” in ji Ayis.

Daya daga cikin wadanda suka amfana da aikin, Success Eliminian, ta yaba wa AGILE bisa sauya dabi’u da al’adun al’umma tare da bunkasa ilimin ’yan mata.

“Aikin AGILE yana sauya tunanin al’umma da al’adunmu. Ya shafe mu ta hanyar ba mu ilmi da da yadda zamu kulada kanmu akan kowane irin kalubale,” In ji ta.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ya ya AGILE Gwamnatin Duniya Hanyar Rayuwar Sauya Bankin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda

Fadar  gwamnatin kasar Iraki ta sanar da cewa ba ta masaniya akan yadda aka shigar da sunayen Ansarullah na Yemen da kuma Hizbullah ta kasar Lebanon a cikin jerin sunayen kungiyoyin ‘Yan ta’adda da aka rike kudadensu dake bankunan kasar.

Bayanin fadar gwamnatin kasar ta Iraki ya kuma kara da cewa; Matakai irin wadannan da ake dauka a kasar ba a aike wa da su zuwa fadar shugaban kasa,abinda ake aikewa fadar shi ne dokokin da majalisar dokokin kasar ta yi, domin a sake tantancewa da kuma amincewa.”

Haka nan kuma sanarwar ta ce; wasu daga cikin abubuwan da ake aikewa fadar mulkin kasar sun hada da tsare-tsaren fadar shugaban kasa,amma abinda ya shafi matakan majalisar ministoci, da na kwamitin dake dakatar da kudaden ‘yan ta’adda da na kwamitin da yake sa ido akan masu wanke kudaden haram, ba a aikewa fadar gwamatin kasar.”

A karshe bayanin ya ce, fadar gwamantin kasar ba ta da wata masaniya akan matakan da aka dauka na bayyana Ansrullah da Hizbullah a matsayin kungiyoyin ‘yan ta’adda tare da daukar matakan hana amfani da kudadensu a cikin bankunan kasar ta Iraki.

Sanarawar da aka yi a kasqar Iraki a shekarun jiya Alhamis na cewa an hana wasu kungiyoyi da su ka hada “Isis, alka’ida, Ansarullah da kuma Hizbullah, amfani da bankunan kasar domin hada-hadar kudade, ya tayar da kura a cikin da wajen kasar. Mutane sun fito kan titutan kasar ta Iraki domin yin tir da wannan sanarwa.

Sai dai daga baya gwamantin kasar ta janye wannan sanarwa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa December 6, 2025 Iran Da Pakisatan Sun Amince Da Farfado da Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad December 5, 2025 Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya December 5, 2025 Trump Ya Yabawa Rwanda Da Kongo DMK Kan Sulhuntawa A Yakin Gabancin Kongo December 5, 2025 Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu December 5, 2025 Shin Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump? December 5, 2025 Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha December 5, 2025 Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump December 5, 2025 Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Taimaka Wa Laifukan Isra’ila A Kan Falasdinawa December 5, 2025 Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania December 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika
  • Mata ‘yar wasan harbi ta Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya a karo na 4
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike