An Kashe Sojojin HKI 2 A Yammacin Kogin Jordan
Published: 4th, February 2025 GMT
Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa, an kashe sojoji 2 a yankin kusa da Tubas dake Arewacin yammacin kogin Jordan.
Kafafen watsa labarun sun kuma ce, maharin ya isa wani shinge na soja dake kusa da Tayasir, ya kuma boye a cikin hasumiyar da masu tsaro ke zama a ciki, sannan ya bude wa sojoji wuta daga sama.
Har ila yau maharin ya yi bata-kashi da sojojin da suke a wajen, sai dai a karshe sun ci karfinsa, da hakan ya yi shahadarsa.
A bayanin da kungiyar Hamas ta fitar ta jininawa maharin tare da cewa, abinda hakan yake nufi shi ne cewa hare-haren da ‘yan sahayoniya suke kai wa ba za su tafi haka kawai ba tare da mayar da martani ba.
Ita ma kungiyar “ Jabahatu-tahrir Falasdin” ta sanar da cewa; Harin yana kara tabbatar da cewa, tsaron ‘yan mamaya yana da rauni, kuma ba za ta iya jurewa a gaban gwgawarmaya ba.
Wannan harin dai yana zuwa ne a lokacin da ‘yan sahayoniya suke cigaba da yi wa al’ummar Falasdinu kisan kiyashi da kuma barnata gidajensu.
A ranar Litinin din da ta gabata, sojojin mamayar sun kashe Falasdinawan da sun kai 70 a sansanin ‘yan hijira na Jenin. Dama tun a ranar Asabar sojojin HKI sun rusa gidajen Falasdinawa da sun kai 100 a sansanin na Jenin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
Kungiyar Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa kasar Gabon tare da maida ta a cikin cibiyoyinta.
AU, ta sanar da hakan ne yayin taron kwamitin zaman lafiya da tsaro na kungiyar yau Laraba a Addis Ababa.
Hakan dai ya karshen dakatarwar da aka yi wa kasar ta Gaban daga kungiyar, watanni 20 bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Agustan 2023.
Kwamitin zaman lafiya da tsaro na AU, ya yi la’akari da mika mulki da ya hambarar da Ali Bongo “gaba daya cikin nasara,” saboda haka ya yanke shawarar dage takunkumin nan take.
‘’Tsarin siyasar Gabon yana da ” gamsarwa” inji sanarwar kungiyar.
Wannan matakin na AU ya zo ne kwanaki uku gabanin rantsar da Janar Brice Oligui Nguema, wanda aka zaba a matsayin shugaban kasar a ranar 12 ga Afrilu.