HausaTv:
2025-06-22@01:13:59 GMT

 An Kashe Sojojin HKI 2 A Yammacin Kogin Jordan

Published: 4th, February 2025 GMT

Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa, an kashe sojoji 2 a yankin kusa da Tubas dake Arewacin yammacin kogin Jordan.

Kafafen watsa labarun sun kuma ce,  maharin ya isa wani shinge na soja dake kusa da Tayasir, ya kuma boye a cikin hasumiyar da masu tsaro ke zama a ciki, sannan ya bude wa sojoji wuta daga sama.

Har ila yau  maharin ya yi bata-kashi da sojojin da suke a wajen, sai dai a karshe sun ci karfinsa, da hakan ya yi shahadarsa.

A bayanin da kungiyar Hamas ta fitar ta jininawa maharin tare da cewa, abinda hakan yake nufi shi ne cewa hare-haren da ‘yan sahayoniya suke kai wa ba za su tafi haka kawai ba tare da mayar da martani ba.

Ita ma kungiyar  “ Jabahatu-tahrir Falasdin” ta sanar da cewa; Harin yana kara tabbatar da cewa, tsaron ‘yan mamaya yana da rauni, kuma ba za ta iya jurewa a gaban gwgawarmaya ba.

Wannan harin dai yana zuwa ne a lokacin da ‘yan sahayoniya suke cigaba da yi wa al’ummar Falasdinu kisan kiyashi da kuma barnata gidajensu.

A ranar Litinin din da ta gabata, sojojin mamayar sun kashe Falasdinawan da sun kai 70 a sansanin ‘yan hijira na Jenin. Dama tun a ranar Asabar sojojin HKI sun rusa gidajen Falasdinawa da sun kai 100 a sansanin na Jenin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

Manyan kungiyoyin kwallon kafa a Turai Tottenham Hotspur da West Ham United na fafatawa wajen ganin sun dauki tauraron dan wasan Nijeriya dake buga kwallo a Club Brugge, Raphael Onyedika, ana alakanta Onyedika da barin kungiyar Club Brugge sakamakon rawar gani da ya taka a bana.

Dan wasan na Nijeriya ya samu dimbin masu sha’awar raba shi da Brugge saboda bajintar da ya nuna a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai ta bara, a cewar Transferfeed, kungiyoyin biyu na son siyan dan wasan tsakiyar a wannan bazarar, West Ham na son ya maye gurbin Tomas Soucek dan kasar Czech, wanda ke kan hanyarsa ta barin kungiyar.

Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6 Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

A daya bangaren kuma kungiyar Tottenham na son kara yawan yan wasanta na tsakiya bayan ta kare a mataki na 16 a gasar Firimiya a kakar wasan da ta gabata, hakazalika babbar kungiyar kwallon kafa ta AC Milan ta nuna sha’awarta ta sayen dan wasan mai shekaru 24, kadan ya rage Onyedika ya bar Brugge zuwa kungiyar Galatasaray ta Turkiyya a bazarar da ta gabata amma kuma sai ya ci gaba da zama a kungiyar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika
  • Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa
  • Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal