An Kashe Sojojin HKI 2 A Yammacin Kogin Jordan
Published: 4th, February 2025 GMT
Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa, an kashe sojoji 2 a yankin kusa da Tubas dake Arewacin yammacin kogin Jordan.
Kafafen watsa labarun sun kuma ce, maharin ya isa wani shinge na soja dake kusa da Tayasir, ya kuma boye a cikin hasumiyar da masu tsaro ke zama a ciki, sannan ya bude wa sojoji wuta daga sama.
Har ila yau maharin ya yi bata-kashi da sojojin da suke a wajen, sai dai a karshe sun ci karfinsa, da hakan ya yi shahadarsa.
A bayanin da kungiyar Hamas ta fitar ta jininawa maharin tare da cewa, abinda hakan yake nufi shi ne cewa hare-haren da ‘yan sahayoniya suke kai wa ba za su tafi haka kawai ba tare da mayar da martani ba.
Ita ma kungiyar “ Jabahatu-tahrir Falasdin” ta sanar da cewa; Harin yana kara tabbatar da cewa, tsaron ‘yan mamaya yana da rauni, kuma ba za ta iya jurewa a gaban gwgawarmaya ba.
Wannan harin dai yana zuwa ne a lokacin da ‘yan sahayoniya suke cigaba da yi wa al’ummar Falasdinu kisan kiyashi da kuma barnata gidajensu.
A ranar Litinin din da ta gabata, sojojin mamayar sun kashe Falasdinawan da sun kai 70 a sansanin ‘yan hijira na Jenin. Dama tun a ranar Asabar sojojin HKI sun rusa gidajen Falasdinawa da sun kai 100 a sansanin na Jenin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Jinjinawa Gwamnan Jigawa Bisa Ayyukan Ci Gaban Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Ministan Yada Labarai Alhaji Mohammed Idris, ya yabawa Gwamna Malam Umar Namadi bisa jagoranci na gaskiya da tsari, yana mai cewa Jihar Jigawa ta zama abin koyi wajen gudanar da mulki da kuma ingantaccen aiki a ma’aikatu.
Ministan ya yi wannan yabo ne lokacin wata ziyarar ban girma da ya kai wa gwamnan a Gidan Gwamnati da ke Dutse.
Muhammad Idris ya tuna da wata ziyarar da ya taba kaiwa Jigawa a baya, lokacin da ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya domin duba harkokin noma. Ya ce yadda ya ga ana yin noman rani ya sa shi shauki game da irin ci gaban da ake samu a jihar.
Ya kuma bayyana godiyarsa kan kyakkyawan tarba da tawagarsa ta samu, yana mai cewa Jigawa jiha ce mai mutunci, zumunci da karimci.
Ministan ya kara tabbatar da aniyar gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu wajen magance matsalolin tsaro da tattalin arziki, musamman ta hanyar gyaran da ake yi a rundunar tsaro domin tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.
A jawabinsa, Gwamna Namadi ya yi maraba da ministan da tawagarsa, yana mai bayyana cewa taron matasan APC na Arewa maso Yamma wata dama ce ta musayar ra’ayi game da mulki, ci gaba da kuma bunkasar matasa.
Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen bunkasa karkokin matasa da mata a cikin tsarin shirye shiryenta na cigaban jihar.
“Muna goyon bayan mulikin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, Mutanen Jigawa suna tare da shi, muna goyon bayan shirin sa na ‘Renewed Hope’ domin gina Najeriya mai da hadin kai,” in ji gwamnan.
Daga nan sai gwamnan tare da ministoci suka halarci taron matasan APC na Arewa maso Yamma a Dutse, inda aka tattauna batutuwan shugabanci, gudunmawar da matasa ke badawa, da ci gaba mai dorewa.