HausaTv:
2025-05-01@03:38:37 GMT

 An Kashe Sojojin HKI 2 A Yammacin Kogin Jordan

Published: 4th, February 2025 GMT

Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa, an kashe sojoji 2 a yankin kusa da Tubas dake Arewacin yammacin kogin Jordan.

Kafafen watsa labarun sun kuma ce,  maharin ya isa wani shinge na soja dake kusa da Tayasir, ya kuma boye a cikin hasumiyar da masu tsaro ke zama a ciki, sannan ya bude wa sojoji wuta daga sama.

Har ila yau  maharin ya yi bata-kashi da sojojin da suke a wajen, sai dai a karshe sun ci karfinsa, da hakan ya yi shahadarsa.

A bayanin da kungiyar Hamas ta fitar ta jininawa maharin tare da cewa, abinda hakan yake nufi shi ne cewa hare-haren da ‘yan sahayoniya suke kai wa ba za su tafi haka kawai ba tare da mayar da martani ba.

Ita ma kungiyar  “ Jabahatu-tahrir Falasdin” ta sanar da cewa; Harin yana kara tabbatar da cewa, tsaron ‘yan mamaya yana da rauni, kuma ba za ta iya jurewa a gaban gwgawarmaya ba.

Wannan harin dai yana zuwa ne a lokacin da ‘yan sahayoniya suke cigaba da yi wa al’ummar Falasdinu kisan kiyashi da kuma barnata gidajensu.

A ranar Litinin din da ta gabata, sojojin mamayar sun kashe Falasdinawan da sun kai 70 a sansanin ‘yan hijira na Jenin. Dama tun a ranar Asabar sojojin HKI sun rusa gidajen Falasdinawa da sun kai 100 a sansanin na Jenin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon

Kungiyar Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa kasar Gabon tare da maida ta a cikin cibiyoyinta.

AU, ta sanar da hakan ne yayin taron kwamitin zaman lafiya da tsaro na kungiyar yau Laraba a Addis Ababa.

Hakan dai ya karshen dakatarwar da aka yi wa kasar ta Gaban daga kungiyar, watanni 20 bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Agustan 2023.

Kwamitin zaman lafiya da tsaro na AU, ya yi la’akari da mika mulki da ya hambarar da Ali Bongo “gaba daya cikin nasara,” saboda haka ya yanke shawarar dage takunkumin nan take.

‘’Tsarin siyasar Gabon yana da ” gamsarwa” inji sanarwar kungiyar.

Wannan matakin na AU ya zo ne kwanaki uku gabanin rantsar da Janar Brice Oligui Nguema, wanda aka zaba a matsayin shugaban kasar a ranar 12 ga Afrilu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114