Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa
Published: 5th, March 2025 GMT
Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya zayyana wasu muhimman abubuwan da ya kamata mai azumi ya lazimta a watan Ramadan.
Yayin da al’ummar Musulmi ke gudanar da ibadar azumi, Sheikh Daurawa ya bayyana cewa akwai ɗimbin lada ga duk wanda ya aiwatar da waɗannan ayyuka:
Kwamitin majalisa ya yi watsi da ƙorafin Natasha a kan Akpabio Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata1.
Azumi: Mai azumi ya kula da azuminsa, ya san hukunce-hukuncensa, ya kiyaye su, tare da nisantar abin da zai rage lada ko karya azumi.
2. Sallah: Ya fi dacewa a dage da Sallar Taraweeh da Tahajjud, tare da yin sallolin farilla a cikin jam’i da nafiloli da ake yi kafin ko bayan su.
3. Ciyarwa: Ciyarwa tana da matuƙar muhimmanci, ko da dabino ko ruwan sanyi ne. “Domin Annabi (SAW) ya ce, duk wanda ya ciyar da mai azumi, za a ƙara masa lada kamar ya yi wani azumin ne,” in ji Sheikh Daurawa.
4. Umrah: Idan mutum yana da hali, yana da lada mai girma yin Umrah a watan Ramadan. Idan kuwa ba shi da hali, sai ya maye gurbinsa da ciyarwa.
5. I’tiƙafi: Sheikh Daurawa ya shawarci Musulmi da su mayar da hankali wajen shiga I’tiƙafi, idan suna da hali, domin yin ibada tare da nesantar shagalin duniya.
6. Daren Lailatul Ƙadar: Ya buƙaci Musulmi da su dage da neman dacewa da daren Lailatul Ƙadar ta hanyar yin salloli, addu’o’i, da sauran ayyukan alheri.
7. Yafiya: Sheikh Daurawa ya buƙaci Musulmi da su yafe wa juna, domin neman gafarar Allah a cikin wannan wata mai alfarma.
8. Karatun Al-Ƙur’ani: Ya ce ya dace Musulmi su dage da yawaita karatun Al-Ƙur’ani, domin a watan Ramadan aka saukar da shi.
9. Addu’a: Yana da muhimmanci a dage da yin addu’a, musamman a lokacin Sahur, lokacin buɗa-baki, da lokacin da ake cikin azumi, domin a waɗannan lokuta Allah na karɓar addu’o’i.
10. Zumunci: Sada zumunta a watan Ramadan yana ƙara albarka, arziƙi, da zaman lafiya, kamar yadda Sheikh Daurawa ya bayyana.
11. Tausayi: Azumi yana koyar da tausayi da taimako, domin mai azumi zai jin halin da masu buƙata ke ciki, hakan zai sa ya fi jin ƙansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Al Ƙurani Ramadan Sheikh Daurawa Tausayi Sheikh Daurawa ya a watan Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
Yayin da damina ke ƙara ƙaratowa, Gwamnatin Jihar Kano, ta fara wani aikin tsaftace manyan magudanan ruwa domin daƙile aukuwar ambaliyar ruwa.
An fara aikin ne a yankin shataletalen Baban Gwari, ɗaya daga cikin wuraren da ambaliya ke yawan aukuwa a Birnin Kano.
Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A NajeriyaMa’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ce ke jagorantar aikin tsaftace magudanan ruwan.
Wannan mataki na daga cikin shirin gwamnatin jihar na kare rayuka, dukiyoyi, da kuma inganta ababen more rayuwa.
A lokacin ƙaddamar da aikin, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Hashim Muhammad Dahiru, ya bayyana cewa an zaɓi Baban Gwari saboda muhimmancinsa da kuma yadda wajen yake a lokacin damina.
Ya ce wajen ya daɗe da zama wajen zubar da shara barkatai da kuma toshe hanyoyin ruwa.
Ya ƙara da cewa wannan wajen ba wai kawai muhimmiyar mahaɗa ba ce, amma kuma yana ɗaya daga cikin manyan hanyoyin ruwa da ke da alaƙa da ruwan Jakara da Kwarin Gogau.
Kwamishinan ya bayyana cewa mazauna yankin da masu wucewa sun sha fuskantar ambaliya da ta shafi rayuwarsu, lafiyarsu da kuma zirga-zirgarsu.
Ya ce wannan aikin ba na al’ada ba ce, illa alama ce da ke nuna cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin kare muhalli da kuma samar da birni mai jure sauyin yanayi da ambaliya.
Ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jagoranci da goyon bayan da ya bai wa ma’aikatar wajen aiwatar da wannan aiki.
Ya ce gwamnatin ta amince da sanya tsaftace magudanan ruwa a matsayin aikin da za a riƙa gudanarwa a kowace shekara domin tabbatar da tsaftar hanyoyin ruwa a faɗin jihar.
Haka kuma, gwamnatin ta bayar da kwangilar gyaran shataletalen Baban Gwari domin inganta zirga-zirga da rage yawan ambaliya, ta hanyar gina sabbin hanyoyin ruwa.
Kwamishinan ya bayyana cewa waɗannan matakai suna nuna irin hangen nesa da damuwar gwamnan jihar kan lafiyar jama’a da kuma kare su daga illolin da ke zuwa da ambaliya da sauyin yanayi.
Ya buƙaci jama’a da su daina zubar da shara barkatai, musamman a cikin magudanan ruwa, ya kuma buƙaci su riƙa ɗaukar nauyin tsaftace muhallinsu.
Ya ce gwamnatin za ta yi nata aikin, amma ana buƙatar haɗin gwiwar kowa da kowa domin a cimma nasara.
Ya kuma buƙaci ma’aikata da abokan aikin muhalli da su gudanar da aikinsu da kulawa da gaskiya, yana mai cewa aikin ba wai tsaftace magudanan ruwa ba ne kawai, amma aikin ne na kare rayuka, daƙile haɗura da kuma gina sabuwar Kano mai tsafta da lafiya.
A ’yan shekarun nan, yankin Baban Gwari ya yi ƙaurin suna wajen yawan aukuwar ambaliya, har ma da rasa rayuka da dukiyoyi.
Wannan ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa domin magance matsalar kafin saukar daminar bana.