Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa
Published: 5th, March 2025 GMT
Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya zayyana wasu muhimman abubuwan da ya kamata mai azumi ya lazimta a watan Ramadan.
Yayin da al’ummar Musulmi ke gudanar da ibadar azumi, Sheikh Daurawa ya bayyana cewa akwai ɗimbin lada ga duk wanda ya aiwatar da waɗannan ayyuka:
Kwamitin majalisa ya yi watsi da ƙorafin Natasha a kan Akpabio Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata1.
Azumi: Mai azumi ya kula da azuminsa, ya san hukunce-hukuncensa, ya kiyaye su, tare da nisantar abin da zai rage lada ko karya azumi.
2. Sallah: Ya fi dacewa a dage da Sallar Taraweeh da Tahajjud, tare da yin sallolin farilla a cikin jam’i da nafiloli da ake yi kafin ko bayan su.
3. Ciyarwa: Ciyarwa tana da matuƙar muhimmanci, ko da dabino ko ruwan sanyi ne. “Domin Annabi (SAW) ya ce, duk wanda ya ciyar da mai azumi, za a ƙara masa lada kamar ya yi wani azumin ne,” in ji Sheikh Daurawa.
4. Umrah: Idan mutum yana da hali, yana da lada mai girma yin Umrah a watan Ramadan. Idan kuwa ba shi da hali, sai ya maye gurbinsa da ciyarwa.
5. I’tiƙafi: Sheikh Daurawa ya shawarci Musulmi da su mayar da hankali wajen shiga I’tiƙafi, idan suna da hali, domin yin ibada tare da nesantar shagalin duniya.
6. Daren Lailatul Ƙadar: Ya buƙaci Musulmi da su dage da neman dacewa da daren Lailatul Ƙadar ta hanyar yin salloli, addu’o’i, da sauran ayyukan alheri.
7. Yafiya: Sheikh Daurawa ya buƙaci Musulmi da su yafe wa juna, domin neman gafarar Allah a cikin wannan wata mai alfarma.
8. Karatun Al-Ƙur’ani: Ya ce ya dace Musulmi su dage da yawaita karatun Al-Ƙur’ani, domin a watan Ramadan aka saukar da shi.
9. Addu’a: Yana da muhimmanci a dage da yin addu’a, musamman a lokacin Sahur, lokacin buɗa-baki, da lokacin da ake cikin azumi, domin a waɗannan lokuta Allah na karɓar addu’o’i.
10. Zumunci: Sada zumunta a watan Ramadan yana ƙara albarka, arziƙi, da zaman lafiya, kamar yadda Sheikh Daurawa ya bayyana.
11. Tausayi: Azumi yana koyar da tausayi da taimako, domin mai azumi zai jin halin da masu buƙata ke ciki, hakan zai sa ya fi jin ƙansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Al Ƙurani Ramadan Sheikh Daurawa Tausayi Sheikh Daurawa ya a watan Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
Shugaban Palasdinu da kuma kungiyar kwatar yencin falasdinawa PLO Mahmud Abbas ya nada magajinsa da kuma wasu mataimaka.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran, ta bayyana cewa Abbas dan shekara 89 ya nada mataimakinsa ne bayan taron majalisar gudanarwa ta gwamnatinsa a makon da ya gabata.
Labarin ya kara da cewa kasashen yamma da yankin sun dade suna takurawa Abbas kan ya nada mataimaki da kuma wasu mataimaka sabuda rawar da gwamnatinsa zata taka bayan yakin gaza.
A yau ne majalisar zartarwa ta amince da nada Hussein Al Sheikh a matsayin mataimakin shugaban majalisar da kuma mataimakin shugaban kasa a lokaci guda.
Kamfanin dillancin labarai na gwamnatin Falasdinawan WAFA, ya bayyana cewa gwamnatin Abbas ce da hakkin sa hannu a kan yarjeniyoyi da suka shafi Falasdinu, a madadin dukkan kungiyoyin Falasdinawa, banda wadanda su ka dauke da makamai suna yakar HKI, wato Hamas da kuma Jihadul Islami a Gaza.
Mr Al Sheikh, dan shekara 64 a duniya na hannun daman Abbas ne a kungiyarsa ta fatah.