HausaTv:
2025-04-30@21:01:07 GMT

Kungiyar “Amnesty” Na Zargi Netanyahu Da Aikata Laifukan Yaki

Published: 1st, April 2025 GMT

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa “ Amnesty International” ta zargi fira ministan HKI da cewa, mai aikata laifin yaki ne, da kuma amfani da yunwa a matsayin makamin yaki akan fararen hula.

Kungiyar ta kare hakkin bil’adama ta bayyana cewa a cikin ganganci Netanyahu yake kai wa fararen hula harer-hare da kuma aikata laifuka akan bil’adama.

Haka nan kuma kungiyar ta yi gargadi akan ziyarar da Netanyahu zai kai wata kasa daga cikin wadanda su ka rattaba hannu a yarjejeniyar kafa kotun duniya ba tare da an kama shi ba. Kungiyar “Amnesty Interational” ta ce rashin kama Fira ministan na HKI zai kara ba shi karfin gwiwar ci gaba da aikata laifuka.

Dangane da gayyatar da kasar Hungary ta yi wa Netanyahu ya ziyarce ta, kungiyar Amnesty International’ ta bayyana shi da cewa cin zarafin dokokin kasa da kasa ne rena kotun, tana mai yin kira ga gwmanatin wannan kasar da cewa, da zarar ya isa, su damke shi, su mika shi ga kotun manyan laifuka ta kasa da kasa.

Fira ministan HKI zai kai ziyara zuwa kasar Hungary ne da take daya daga cikin wadanda su ka rattaba hannu akan yarjejeniyar Roma da ta kai ga kafuwar kotun manyan laifukan ta kasa da kasa. Ofishin Fira ministan ‘yan sahayoniyar ya ce, zaiyarar za ta dauki kwanaki biyar, zai kuma gana da takwaranta na wannan kasa Victor Orban.

Kotun kasa da kasa ta manyan laifuka ta fita da sammacin a kamo mata fira ministan HKI Benjemine Netanyahu saboda aikata laifukan yaki akan al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 

Shi ma dayan, bayan ya bayyana cewa, sun kasance barayin mota ne a jihar Katsina amma wani abokinsu ya gayyace su zuwa jihar Filato domin ci gaba da sana’ar.

 

 Yayin da ya amince zai jagoranci Tawagar Soji zuwa maboyarsu, jami’an sun gano bindiga kirar fistul daya da mukullai da suke amfani da su wajen bude motoci da gidajen jama’a, inda daga bisani shi ma ya yi kokarin arcewa kamar yadda abokin shi ya yi. Hakan ta sa shi ma aka harbe shi har lahira.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa