Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
Published: 31st, October 2025 GMT
A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara
Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna
Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya
Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.                
      
				
Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: a jihar Katsina
এছাড়াও পড়ুন:
An kai ƙarar malamai 2 kan zargin ɓatanci ga Annabi a Kaduna
Wata gamayyar malaman addinin Musulmai ƙarƙashin inuwar Concerned Ulama of Sunnah ta aika da ƙorafi zuwa ga Gwamnatin Jihar Kaduna tana zargin wasu malamai biyu da yin ɓatanci ga Annabi Muhammad (S.A.W).
Ana zargin malaman ne da yi batancin a cikin wa’azozinsu na kafafen sada zumunta.
Gwamnatin Kamaru za ta gurfanar da Issa Tchiroma a kotu kan zargin tayar da zaune tsaye Uwa da ’yarta sun nitse a hatsarin jirgin ruwa a BornoƘorafin, wanda malamai goma sha shida (16) suka sanya wa hannu, ƙarƙashin jagorancin Shaikh Umar Shehu Zaria da Malam Muhammad Sani Abubakar, Babban Limamin Masallacin Juma’a na Hayin Na’iya, ya bukaci gwamnatin jihar da ta gaggauta ɗaukar mataki.
A cewar masu ƙorafin, ayyukan waɗannan malamai biyu “na iya janyo tashin hankali a ƙasarmu mai albarka idan aka bar su haka.”
Sun roƙi hukumomi da su gayyace su domin tattaunawa idan ya zama dole, ko kuma su dakatar da su, suna gargaɗin cewa rashin ɗaukar mataki “na iya haifar da tashin hankali da rikici wanda gwamnati ba za ta so hakan ba.”
Kungiyar ta bayyana cewa batun ya wuce na son rai, yana da alaƙa kai tsaye da muhimman ƙa’idodin addinin Musulunci.
“Akwai imani na asali cikin al’ummar Musulmi na girmamawa da kare mutuncin Annabi Muhammad (S.A.W). Shi ne asalin alheri ga kowanne Musulmi a duniya da lahira,” in ji ƙorafin”
Masu ƙorafin sun ambaci shari’ar Musulunci da maganganun manyan malamai dake nuna tsananin laifin batanci ga Annabi.
Sun kuma roƙi gwamnatin jihar da ta gaggauta ɗaukar mataki don hana rikici.
“Jihar Kaduna ta sha fama da rikice-rikicen ƙabilanci da na addini a baya, amma da taimakon Allah da jajircewar gwamnati, an shawo kan da dama daga cikin lamarin,” in ji su.
A martanin da ya bayar, Daraktan Hukumar Huldar Addinai ta Jihar Kaduna, Tahir Umar Tahir, ya tabbatar da karɓar ƙorafin kuma ya tabbatar wa malamai cewa gwamnati za ta duba shi.
“Mun karɓi ƙorafinsu a madadin Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, kuma da yardar Allah za mu duba wannan batu. Za a ɗauki matakan da suka dace don hana tashin hankali,” in ji Kwamishinan.
Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ci gaba da tsayawa wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai tsakanin addinai:
Tahir ya kuma roƙi shugabannin da malaman addinai da su yi hattara a cikin wa’azozinsu, yana gargaɗin su guji duk wani saƙo da zai iya haddasa rarrabuwar kai ko tashin hankali a cikin jihar.
 Bafarawa Ya Kaddamar Da Wata Kungiya Mai Suna “Arewa Cohesion Initiative” Don Maganin Kalubalen Da Yankin Arewa Ke Fuskanta
Bafarawa Ya Kaddamar Da Wata Kungiya Mai Suna “Arewa Cohesion Initiative” Don Maganin Kalubalen Da Yankin Arewa Ke Fuskanta