Aminiya:
2025-10-31@23:31:16 GMT

Kotu ta dakatar da babban taron PDP

Published: 31st, October 2025 GMT

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dakatar da jam’iyyar PDP daga gudanar babban taronta na ƙasa da aka shirya yi a Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, a watan gobe.

Mai shari’a James Omotosho ne, ya bayar da wannan umarni, yayin da yake yanke hukunci kan wata ƙara da aka shigar domin sanin ko jam’iyyar PDP na da ikon ci gaba da shirya taron da aka tsara gudanarwa a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.

Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m

Waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Austine Nwachukwu, shugaban PDP na Jihar Imo; Amah Abraham Nnanna, shugaban PDP na Jihar Abiya da Turnah George, sakataren PDP na yankin Kudu maso Kudu.

Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu, Sakataren shirya taruka na jam’iyyar, Umar Bature, Kwamitin Ayyuka na jam’iyyar na Ƙasa (NWC) da Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar na Ƙasa (NEC).

Masu shigar da ƙarar sun kasance ’yan tsahin Nyesom Wike ne.

Sun roƙi kotu da ta hana gudanar da taron, inda suka bayyana cewar jam’iyyar ta saɓa wa dokokinta, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, da kuma Dokar Zaɓe wajen shirya taron.

Lauyansu ya shaida wa kotu cewa: “Ba a gudanar da taron wakilai a jihohi 14 ba don haka shirin taron ya saɓa wa doka.”

Sai dai PDP ta kare kanta, inda ta ce lamarin na harkokin cikin gidan jam’iyyar ne, don haka bai kamata kotu ta tsoma baki ba.

Jam’iyyar ta zargi masu ƙarar da ƙoƙarin tayar da rikici domin hana ta gudanar da sabon zaɓen shugabanni.

Aminiya ta ruwaito cewa wannan rikici ya ƙara dagula al’amura a jam’iyyar PDP.

Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, a baya ya yi zargin cewa an yi amfani da hannunsa na bogi a takardun da aka aike wa INEC game da shirya taron.

Amma shugabancin jam’iyyar ya ƙaryata wannan zargi.

A halin yanzu, Kwamitin Shirya Taron na Ƙasa (NCOC) ya ɗage tantance ’yan takara da aka tsara gudanarwa a ranar 28 ga watan Oktoba.

Mutane da dama na ganin ɗage tantance ’yan takarae na da nasaba da jiran sakamakon hukuncin kotu kafin a ci gaba da shirye-shirye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban taro shirya taron jam iyyar na a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An yi taron musamman na Rasha bisa taken “Kirkire, bude kofa da more Ci Gaba” a ran 27 ga watan nan da muke ciki, wanda babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin wato CMG ya shirya tare da gudanarwa a Moscow.

A cikin jawabinsa ta bidiyo, shugaban CMG, Shen Haixiong, ya bayyana cewa, an kammala cikakken zama na 4 na kwamitin tsakiya na 20 na jam’iyyar kwaminis ta kasar dake jawo hankalin duniya cikin nasara a Beijing. Taron ya sake shelar wa duniya cewa Sin za ta fadada bude kofarta ga duniya, ta kuma bude sabon babi na samun wadata ta hanyar hadin gwiwa. CMG zai ci gaba da gina dandalin tattaunawa na duniya tare da abokan hulda, da aiwatar da shawarwarin duniya 4 da shugaban kasar ya gabatar, da kuma more shiri irin kasar na Sin a bangaren inganta tsarin shugabancin duniya. CMG zai kuma ci gaba da ba da labarin Sin mai kyau ga duniya ta hanyar amfani da karfinta wajen yada labarai, da bayyana damammakin da Sin ke samarwa a duniya.

Bugu da kari, a ranar 27 ga Oktoba, an gudanar da taron musamman na Bahrain a babban birninta Manama, da kuma taron musamman na Hungary a Budapest, duka a kan taken “Kirkire da bude kofa da more Ci Gaba”. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin October 29, 2025 Daga Birnin Sin Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a October 29, 2025 Daga Birnin Sin Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa October 29, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya
  • An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest
  • Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC
  • Gwamnatin Kamaru za ta gurfanar da Issa Tchiroma a kotu kan zargin tayar da zaune tsaye