HausaTv:
2025-06-15@19:45:02 GMT

Faransa : An haramta wa Marie Le Pen, takara har tsawon shekaru 5

Published: 31st, March 2025 GMT

A Faransa, an haramta wa Marie Le Pen yin takara har na tsawon shekaru biyar kuma hakan na nufin ba za ta yi takarar shugabancin kasar ba a shekarar 2027.

An dai samu yar siyasar ne da laifin almubazzaranci da kudaden jama’a wajen daukar nauyin jam’iyyarta ta National Rally mai tsaurin ra’ayi.  

An tuhumi Le Pen tare da wasu manyan yan jam’iyyar tata guda 20 da daukar masu taimaka musu aiki wadanda suka yi wa jam’iyyarta aiki maimakon Majalisar Turai wadda ita ce ke biyan ma’aikatan albashi.

 

Ms Le Pen, mai shekaru 56, ba za ta iya shiga zaben shugaban kasa mai zuwa da aka shirya gudanarwa a shekara ta 2027 ba, inda a yanzu ake ganin ita ce mafi farin jini bayan takara sau uku da ta a yi nasara ba.

Haka kuma an samu wasu ‘yan majalisar wakilai takwas daga jam’iyyarta ta (RN) da laifin wawure dukiyar jama’a.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai

Wasu Hare-haren da gwamnatin Isra’ila ta kai ya haddasa gobara a wasu matatun mai a lardin Bushehr da ke kudancin kasar Iran.

Gobarar ta tashi ne a wurin a ranar Asabar bayan da wasu kananan jiragen yakin Isra’ila guda biyu suka kai hare-hare a kan kayayyakin sarrafa iskar gas da ke yankin kudancin Pars.

Hare-haren sun yi haddassa fashe fashe a matatar iskar gas ta Fajr-e Jam, daya daga cikin mafi girma a Iran, da kuma wata karamar matatar mai a mataki na 14 na tashar iskar gas ta Kudu Pars.

Har yanzu ba a fitar da kiyasin barnar a hukumance ba.

Bayan gobarar, ma’aikatar mai ta Iran ta fitar da wata sanarwa inda ta tabbatar da harin.

Sanarwar ta ce, nan da nan aka kaddamar da aikin shawo kan gobarar da dakile ta.”

Matatar man ta Pars ta kudu ita ce tashar iskar gas mafi girma a duniya, wacce ke kan iyakar teku tsakanin Iran da Qatar.

Ta kunshi sama da kashi 70% na bukatun iskar gas na Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027
  • NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray