Aminiya:
2025-04-30@19:04:13 GMT

Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone

Published: 30th, March 2025 GMT

Rahotanni sun ce, wani ɗan kasar China ya kama matarsa tana cin amanarsa da wanda ya ba ta aiki a lokutan aiki ta hanyar amfani da wata na’urar ɗaukar hoto ta jirgi mara matuƙi da ake sarrafa ta daga nesa, tana leƙen asiri daga nesa.

Mutumin mai hazaka da aka fi sani da Jing ya fara zargin cewa, matarsa na yin wata alaƙa ne bayan ta yi nisa sosai da shi kuma ta canza mu’amalarta sosai, ciki har da ziyartar iyayenta fiye da kowane lokaci da kuma kawo uzuri a duk lokacin da ya yi mata rakiya da kuma ƙarin lokaci a wurin aikinta.

Ladubban Ranar Idin Karamar Sallah Abubuwan da ya kamata Musulmi ya yi a ranar Karamar Sallah

Da yake kokawa kan batun, amma yana tsoron kada ya bayyana kansa ga matarsa idan har zarginsa bai tabbatar ba, Jing ya yanke shawarar yin amfani da na’urar ɗaukar hoto ta jirgi mara matuƙin na haya, don yi wa matarsa leƙen asiri daga nesa.

Yana tuƙa motarsa zuwa wurin aikinta sannan ya kunna jirgin mara matuƙi domin ya duba yankin ba tare da fargabar ganin matarsa ko abokan aikinta ba.

Wata rana yana lura da matarsa, sai ya hango ta fito daga ofishinta tare da wani mutum ta shiga mota da shi.

Sun yi tafiya zuwa wani wuri mai nisa a wajen wasu tsaunuka, inda jirgin mara matuki ya kama su suna rike da hannayensu, suna shiga cikin wani gida mara kyau.

Kusan mintuna 20 suna tare, daga nan sun bar gidan, sun koma wurin aikinsu.

Daga baya Jing ya shiga kafafen sada zumunta na zamani, inda ya bayar da rahoton cewa, mutumin da na’urar jirginsa mara matuki ya dauka a faifan bidiyo wanda da gaske ne ubangidan matarsa ne (wanda take yi wa aiki), kwanan nan ya yi mata karin girma.

“Mutumin da matar ke hulɗa dai shi, shi ne ya ɗauke ta aikin,” inda mijin ya rubuta a shafin sada zumunta na Weibo.

“Haka zalika yana aiki a masana’anta guda da matarsa, don haka bai yi musu dadi ba su ware wani wuri daban don yin alaka a can, saboda haka matata ta tilasta musu haduwa da shi a cikin daji.”

Jing ya kuma wallafa hotunan matarsa da masoyinta suna riƙe da hannayensu, ya kuma ce ya shirya yin amfani da bidiyon da na’urar ta ɗauka a matsayin shaida don neman raba aurensu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kwarto

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa

Ƴan ta’adda da ake zargin Boko Haram ne sun kashe mutane 10 na yawucin dabbobi da kuma mambobin jami’an tsaron sa kai (CJTF) a garin Kwapre, dake cikin ƙaramar hukuma ta Hong a Jihar Adamawa.

Shugaban ƙaramar hukuma, Hon Usman Wa’aganda, ya tabbatar da wannan lamarin ga LEADERSHIP ta waya a ranar Lahadi a Yola, inda ya bayyana cewa wani mutum da ya samu raunuka daga harin ‘yan ta’addan yana samun kulawar likita a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.

Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa

Wa’aganda ya ce ‘yan ta’addan sun ƙone gidaje da dama da kuma amfanin gona, yana mai cewa wannan harin ba na farko bane, domin garin ya sha hare-hare sau da dama wanda ya haifar da asarar rayuka da dukiyoyi.

Ya nemi hukumomin tsaro su ƙara tura jami’ai a yankin domin taimakawa wajen kare al’umma da kuma tabbatar da tsaro.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa