Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone
Published: 30th, March 2025 GMT
Rahotanni sun ce, wani ɗan kasar China ya kama matarsa tana cin amanarsa da wanda ya ba ta aiki a lokutan aiki ta hanyar amfani da wata na’urar ɗaukar hoto ta jirgi mara matuƙi da ake sarrafa ta daga nesa, tana leƙen asiri daga nesa.
Mutumin mai hazaka da aka fi sani da Jing ya fara zargin cewa, matarsa na yin wata alaƙa ne bayan ta yi nisa sosai da shi kuma ta canza mu’amalarta sosai, ciki har da ziyartar iyayenta fiye da kowane lokaci da kuma kawo uzuri a duk lokacin da ya yi mata rakiya da kuma ƙarin lokaci a wurin aikinta.
Da yake kokawa kan batun, amma yana tsoron kada ya bayyana kansa ga matarsa idan har zarginsa bai tabbatar ba, Jing ya yanke shawarar yin amfani da na’urar ɗaukar hoto ta jirgi mara matuƙin na haya, don yi wa matarsa leƙen asiri daga nesa.
Yana tuƙa motarsa zuwa wurin aikinta sannan ya kunna jirgin mara matuƙi domin ya duba yankin ba tare da fargabar ganin matarsa ko abokan aikinta ba.
Wata rana yana lura da matarsa, sai ya hango ta fito daga ofishinta tare da wani mutum ta shiga mota da shi.
Sun yi tafiya zuwa wani wuri mai nisa a wajen wasu tsaunuka, inda jirgin mara matuki ya kama su suna rike da hannayensu, suna shiga cikin wani gida mara kyau.
Kusan mintuna 20 suna tare, daga nan sun bar gidan, sun koma wurin aikinsu.
Daga baya Jing ya shiga kafafen sada zumunta na zamani, inda ya bayar da rahoton cewa, mutumin da na’urar jirginsa mara matuki ya dauka a faifan bidiyo wanda da gaske ne ubangidan matarsa ne (wanda take yi wa aiki), kwanan nan ya yi mata karin girma.
“Mutumin da matar ke hulɗa dai shi, shi ne ya ɗauke ta aikin,” inda mijin ya rubuta a shafin sada zumunta na Weibo.
“Haka zalika yana aiki a masana’anta guda da matarsa, don haka bai yi musu dadi ba su ware wani wuri daban don yin alaka a can, saboda haka matata ta tilasta musu haduwa da shi a cikin daji.”
Jing ya kuma wallafa hotunan matarsa da masoyinta suna riƙe da hannayensu, ya kuma ce ya shirya yin amfani da bidiyon da na’urar ta ɗauka a matsayin shaida don neman raba aurensu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kwarto
এছাড়াও পড়ুন:
Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda ya tattauna ta wayar tarho da jami’ar harkokin waje ta tarayyar turai ya bayyana cewa, ci gaba da tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka ba shi da wata ma’ana, kamata ya yi jami’an tarayyar turai din su yi Allawadai da wuce gona da irin HKI akan Iran.
Da safiyar yau Asabar ne dai jami’ar diplomasiyyar ta turai Kaja Kallas ta kira yi minsitan harkokin wajen jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci inda su ka tattauna halin da ake ciki a yammacin Asiya da ya hada da harin da HKI ta kawo wa Iran.
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana harin na HKI da cewa, wuce gona da iri ne da keta hurumin kasar Iran, kuma harin da ta kai wa cibiyoyin Nukiliya ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama da su ka hada da malaman jami’oi , da kuma mata da kananan yara.
Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi Allawadai da abinda HKI ta yi na take dokokin kasa da kasa.
Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Jamhuriyar musulunci ta Iran ya yi ishara da cewa, kudurin da majalisar alkalai ta hukumar makamashin Nukiliyar Iran ta fitar akan Iran wanda kuma kasashe uku na turai tare da Amurka su ka gabatar da shi, shi ne ya bude wa ‘yan Sahayoniya mashigar da su ka yi amfani da ita wajen wuce gona da iri akan Iran.
A nata gefen babbar jami’ar diplomasiyyar tarayyar turai ta bayyana rashin jin dadinta akan abinda yake faruwa a cikin yankin na yammacin Asiya na rikice-rikice, tare da bayyana cewa suna goyon bayan aiki da diplomasiyya domin tabbatar da zaman lafiya.
A wani labarin mai alaka da wannan kasar Oman ta sanar da cewa, ba za a yi taron da aka shirya yi a tsakanin Iran da Amruka ba.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ce ta fitar da sanarwar cewa; Tattaunawar da aka shirya cewa za a yi a tsakanin Amurka da Iran ba za a yi ta ba a gobe Lahadi.
Ministan harkokin wajen na Oman ya kara da cewa; Diplomasiyya ce kadai ya kamata ta zama hanyar cimma zaman lafiya mai dorewa.