Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone
Published: 30th, March 2025 GMT
Rahotanni sun ce, wani ɗan kasar China ya kama matarsa tana cin amanarsa da wanda ya ba ta aiki a lokutan aiki ta hanyar amfani da wata na’urar ɗaukar hoto ta jirgi mara matuƙi da ake sarrafa ta daga nesa, tana leƙen asiri daga nesa.
Mutumin mai hazaka da aka fi sani da Jing ya fara zargin cewa, matarsa na yin wata alaƙa ne bayan ta yi nisa sosai da shi kuma ta canza mu’amalarta sosai, ciki har da ziyartar iyayenta fiye da kowane lokaci da kuma kawo uzuri a duk lokacin da ya yi mata rakiya da kuma ƙarin lokaci a wurin aikinta.
Da yake kokawa kan batun, amma yana tsoron kada ya bayyana kansa ga matarsa idan har zarginsa bai tabbatar ba, Jing ya yanke shawarar yin amfani da na’urar ɗaukar hoto ta jirgi mara matuƙin na haya, don yi wa matarsa leƙen asiri daga nesa.
Yana tuƙa motarsa zuwa wurin aikinta sannan ya kunna jirgin mara matuƙi domin ya duba yankin ba tare da fargabar ganin matarsa ko abokan aikinta ba.
Wata rana yana lura da matarsa, sai ya hango ta fito daga ofishinta tare da wani mutum ta shiga mota da shi.
Sun yi tafiya zuwa wani wuri mai nisa a wajen wasu tsaunuka, inda jirgin mara matuki ya kama su suna rike da hannayensu, suna shiga cikin wani gida mara kyau.
Kusan mintuna 20 suna tare, daga nan sun bar gidan, sun koma wurin aikinsu.
Daga baya Jing ya shiga kafafen sada zumunta na zamani, inda ya bayar da rahoton cewa, mutumin da na’urar jirginsa mara matuki ya dauka a faifan bidiyo wanda da gaske ne ubangidan matarsa ne (wanda take yi wa aiki), kwanan nan ya yi mata karin girma.
“Mutumin da matar ke hulɗa dai shi, shi ne ya ɗauke ta aikin,” inda mijin ya rubuta a shafin sada zumunta na Weibo.
“Haka zalika yana aiki a masana’anta guda da matarsa, don haka bai yi musu dadi ba su ware wani wuri daban don yin alaka a can, saboda haka matata ta tilasta musu haduwa da shi a cikin daji.”
Jing ya kuma wallafa hotunan matarsa da masoyinta suna riƙe da hannayensu, ya kuma ce ya shirya yin amfani da bidiyon da na’urar ta ɗauka a matsayin shaida don neman raba aurensu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kwarto
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
Mai kuɗin Afrika kuma Shugaban Matatar Mai ta Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya zargi wasu manyan masu harkar mai da shirya maƙarƙashiya domin kashe matatarsa.
Ɗangote ya yi zargin cewa miyagun ’yan kasuwan suna ƙoƙarin kashe matatar mansa mai darajar dala biliyan 20, kamar yadda aka kashe masana’antar tufafi ta ƙasar.
Ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Legas yayin bikin cika shekara ɗaya da fara samar da fetur a matatar, inda ya ce tafiyar ta kasance cike da ƙalubale tun daga farko.
“A gaskiya tafiyar shekara ɗaya da ta wuce ta yi mana matuƙar wuya. Mun zo mu sauya tsarin kasuwancin man ƙasa. Amma wasu na ganin mun raba su da hanayar cin abinci bakinsu,” in ji shi.
’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati BaYa ci gaba da cewa, “Amma abin da muka yi shi ne mun sa Najeriya da nahiyar Afirka gaba ɗaya su yi alfahari.”
Ɗangote ya ce matatar ta riga ta fitar da lita biliyan 1.8 na man fetur zuwa ƙasashen waje cikin watanni uku da suka gabata, sannan tana da isasshen ƙarfi wajen cika buƙatar cikin gida.
Ya ce tun daga fara aikin matatar a watan Satumbar 2024, dogayen layukan man fetur da suka fi shekaru 50 ana fama da su a Najeriya sun zama tarihi.
Ɗangote ya ƙara da cewa farashin fetur ya sauka daga kusan Naira 1,100 zuwa N841 a wasu jihohi, kuma da zarar sabbin motocin gas (CNG) masu dakon mai sun fara aiki a duk faɗin ƙasar, rage farashin zai fi tasiri.
Ya kuma bayyana cewa sabbin motocin CNG 4,000 za su samar da aƙalla ayyukan yi 24,000, ciki har da direbobi, makanikai da sauran ma’aikata.
“Ba mu kore kowa daga aiki ba, sai dai muna ƙara samar da ayyuka,” in ji shi.
Ɗangote ya zargi masu harkar mai da haɗa kai da ’yan kasuwa na cikin gida da na waje da ƙoƙarin hana nasarar matatar.
“Yadda aka hallaka masana’antar yadi, haka suke ƙoƙarin kashe matatar mu,” in ji shi.
A kan zargin cewa bai wadatar da ƙasa da fetur ba, sai ya mayar da martani da cewa: “Idan ba mu da ƙarfin samar da mai, me ya sa muke fitarwa zuwa ƙasashen waje?”
Ya kuma yi ba’a ga Ƙungiyar Ma’aikatan Mai (NUPENG) wadda ta ce rage farashin fetur na matatar Dangote “kyautar Girka ce.” Dangote ya ce: “Ko da kuwa kyautar Girka ce, ai kyauta ce, za ta kuma ci gaba da kasancewa.”
Ya jaddada cewa abin da Najeriya ke buƙata yanzu shi ne kare masana’antunta, domin ci-gaban tattalin arziki da kuma rage dogaro da shigo da kaya daga waje.