Eidl Fitr: Gwamna Dauda Lawal Ya Buƙaci A Samu Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
Published: 30th, March 2025 GMT
Ya ce: “Ya ‘yan uwa Musulmi na Jihar Zamfara da ma sauran wurare, ina miƙa saƙon barka da Sallah tare da taya mu murnar kammala azumin shekarar Hijira ta 1446, wannan wata mai alfarma ta kasance lokaci na sadaukarwa ga Allah (SWT).
“Yayin da muke gudanar da bukukuwan Ƙaramar Sallah, ina kira ga kowannenmu da ya ci gaba da ayyukan ƙwarai, da haƙuri, da karamcin da aka yi a watan Ramadan.
“Ƙalubalan da ke gabanmu suna da yawa kuma suna buƙatar haɗin kai don ganin an magance su, don haka mu ajiye bambance-bambancen da ke tsakaninmu, mu yi aiki tare a matsayin al’umma ɗaya, mu goyi bayan ajandar gwamnati na ceto da sake gina jiharmu.
Gwamna Lawal ya kuma yaba da ƙoƙarin shugabannin addini da na al’umma bisa yadda suke ci gaba da jajircewa wajen samar da zaman lafiya da inganta ɗabi’un da haɗin kan mutane wuri guda.
“Yayin da muke taruwa da masoyanmu domin gudanar da bukukuwan murnar wannan rana, mu sanya jiharmu cikin addu’o’in neman taimakon Ubangiji yayin da muke aiki ba dare ba rana don magance ɗimbin ƙalubalen da ke addabar jihar, Allah SWT ya karbi ibadun mu, ya gafarta mana kurakuran mu, ya kuma albarkaci jiharmu da kasa baki ɗaya tare da samun dawwamammen zaman lafiya da wadatar tattalin arziki. BARKA DA SALLAH”.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, ya amince da nadin Mai Martaba Sarkin Kazaure, Alhaji Dr Najib Hussaini Adamu, a matsayin Amirul Hajj na Jihar Jigawa, kuma shugaban tawagar Gwamnatin jihar domin gudanar da aikin Hajjin 2025.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya sanya wa hannu kuma aka raba wa manema labarai.
Gwamnan ya kuma amince da nadin mambobin tawagar Amirul Hajjin.
Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa, mambobin sun hada da Dr. Yusuf Abdurrahman, Babban Limamin Masarautar Hadejia da Alhaji Lawan Ya’u Roni, Talban Kazaure.
Sauran su ne Dr. Mahmoud Yunusa, Sa’in Dutse da kuma Alhaji Adamu Dauda Zakar, Durbin Hadejia.
Sanarwar ta bayyana cewa an yi wadannan nade-nade ne bisa la’akari da irin kwazon da suka nuna a ayyukansu, sadaukarwa, kishin kasa, amana da kuma tsoron Allah.
A cikin sakon taya murna ga wadanda aka nada, Sakataren Gwamnati ya bukace su da su ci gaba da nuna wadannan dabi’u yayin da za su gudanar da wannan muhimmin aiki da aka dora musu, don kara tabbatar da amanar da gwamnatin da al’ummar Jihar Jigawa suka dora a kansu.
Sanarwar ta kara da cewa, ana sa ran tawagar Amirul Hajjin za ta yi aiki kafada da kafada da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa da kuma sauran hukumomin da suka dace a matakin Jiha, Tarayya da na kasa da kasa domin tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin nasara da inganci.
Sanarwar ta bayyana cewa nade-naden sun fara aiki nan take.
Usman Muhammad Zaria