HausaTv:
2025-11-02@19:36:09 GMT

Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644

Published: 29th, March 2025 GMT

Hukumomi a Myanmar sun ce adadin wadanda suka mutu a girgizar kasar ya kai 1,644, yayin da wasu 3,408 suka jikkata, ye zuwa ranar Asabar din nan.

Tunda farko dai mutane 1,007 ne aka sanar sun mutu sai wasu 2,389 da suka jikkata.

Girgizar mai karfi maki 7.7 ta shafi Kasashen Myanmar da Thailand wadanda suk suka ayyana dokar ta baci a ranar Juma’a.

Tuni kasar Myanmar ta nemi taimakon kasashen duniya da kuma kungiyoyi don agazawa wadanda girgizar kasarta shafa.

Kasar Iran ta ce a shirye take ta taimakawa kasashen biyu da girgizar kasar ta shafa.

A wata sanarwa da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ya fitar yau Asabar ya ce Iran a shirye take ta shiga ayyukan agaji da ceto a kasashen biyu.

Baghai ya kuma jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa da kuma gwamnatoci da al’ummomin kasashen biyu.

Ayyukan agaji na kasa da kasa sun fara kwararowa cikin kasar: masu aikin ceto da agaji da suka hada da barguna, kayan abinci da na bincike, daga kasashen China da Indiya da ke makwabtaka da su, da kuma wasu kasashe.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a girgizar kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Ofishin kula da zirga-zirgar kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin ya ce, an harba kumbon Shenzhou-21 mai dauke da ‘yan sama jannatin kasar Sin 3 cikin nasara, a daren jiya Juma’a, agogon Beijing.

Daga baya kumbon ya sarrafa kansa wajen hade jikinsa da na tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, ta yadda ‘yan saman jannatin suka shiga tashar, inda tsoffin ‘yan saman jannati 3 da suka dade a cikin tashar, suka yi musu maraba. Hakan ya shaida haduwar sabbi da tsoffin ‘yan sama jannatin kasar Sin karo na 7 a tashar binciken sararin samaniya ta kasar.

Bisa shirin da aka yi, wadannan ‘yan sama jannati 6 za su kwashe kimanin kwanaki 5 suna aiki tare a cikin tashar, kafin tsoffin ‘yan saman jannatin 3 su kama hanyar dawowa gida.

Zuwa yanzu, kasar Sin ta riga ta tura ‘yan sama jannati 44 zuwa sararin samaniya. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung  November 1, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik November 1, 2025 Daga Birnin Sin CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma