Aminiya:
2025-11-02@21:10:41 GMT

Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda

Published: 31st, March 2025 GMT

Wani yaro dan shekara hudu da ya kira wayar salular ’yan sandan yankin Mount Pleasant a Karamar Hukumar Charleston Jihar South Carolina da ke Amurka ya ce, mahaifiyarsa ta shanye masa ‘ice cream’ dinsa kuma yana bukatar a hukunta ta, a kai ta gidan yari saboda aikata hakan.

A cewar ’yan sanda yaron dan shekara 4 ya yi kururuwa, inda ya kira ’yan sanda bayan mahaifiyarsa ta shanye masa ice cream dinsa.

Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano

Al’amarin ya faru ne a cikin a garin Mount Pleasant, Wisconsin — mai nisan kilomita bakwai, yamma da Racine — lokacin da yaro dan shekara 4 ya tuntubi ‘yan sanda, inda ya ce, mahaifiyarsa ba ta kyauta masa ba, a cewar wata sanarwa da ’yan sandan kauyen Mount Pleasant suka fitar.

“An aika jami’an ’yan sanda, wato Gardinier da Ostergaard don amsa kiran mai korafin neman agajin jami’an 911, wanda ya bayyana cewa, mahaifiyarsa ba ta kyauta masa kuma yana bukatar a kai ta gidan yari”, in ji hukumomi.

Lokacin da jami’ai suka isa gidansu, yaron ya ce, mahaifiyarsa ta shanye masa ‘ice cream’ dinsa kuma yana bukatar a ka ita gidan yari saboda aikata hakan.

Daga bisani ya kuma shaida wa ’yan sanda cewa, ba ya son a kai mahaifiyarsa gidan yari kawai, yana son a biya shi ‘icecream’ da ta shanye masa.

Daga baya jami’an sun bar gidan bayan sun gano cewa, wannan shi ne dalilin da ya sa aka kira su, amma sun dawo washegari, wanda a wannan karon suka ba wa yaron mamaki, inda suka kawo masa ice cream, “bayan ya yanke shawarar cewa ba ya son mahaifiyarsa ta shiga matsala,” in ji ’yan sanda.

Jami’an ’yan sandan da suka amsa kiran, ba su kaɗai ne suka gano abin dariya game da lamarin ba.

“Ban ce yana da gaskiya ba. Abin da nake fada shi ne na fahimta,” in ji wani mutum da ke mayar da martani ga ofishin ’yan sanda na kauyen Mount Pleasant game da lamarin a shafukan sada zumunta na zamani.

“Aƙalla ya san yadda ake kiran lambar taimako ko neman agajin jami’an tsaro,” in ji wata. “Zai iya ceton ran wani wata rana!”

Jami’an ’yan sandan da suka ziyarci gidan su yaron sun dauki hoto tare da yaron mai shekara 4 bayan an warware matsalar, inda suka samu damar yin barkwanci.

“Ina son jin labarin jami’anmu game da abin ban mamaki, inda suke samar da kyakkyawar dangantaka tsakaninsu da yara,” in ji wani mai amfani da kafofin sada zumunta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yaro mahaifiyarsa ta

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya shawarci Shugaba Bola Tinubu da ya ɗauki mataki mai tsauri a kan Shugaban Amurka, Donald Trump, game da barazanar da ya yi na amfani da ƙarfin soja a kan Najeriya.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Lahadi, malamin ya bayyana cewa irin wannan magana ta Trump cin mutunci ce ga ’yancin Najeriya.

Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka

Don haka malamin ya yi kira da a ɗauki matakin diflomasiyya cikin gaggawa.

“Trump ya yi barazana ga ƙasa mai cin gashin kanta da harin soja, wannan girmamawa ne ga ƙasarmu,” in ji Gumi.

Sheikh Gumi, ya nemi Gwamnatin Tarayya ta kira Jakadan Amurka domin neman bayani da kuma a janye wannan barazanar, inda ya yi gargaɗin cewa idan ba a yi haka ba, to Najeriya ta yanke hulɗa da Amurka.

“Shugaba Tinubu ya kamata ya kira Jakadan Amurka idan ba su janye barazanar ba, to mu yanke hulɗa da wannan gwamnati mara mutunci,” in ji shi.

Gumi, ya kuma jaddada cewa Najeriya tana da damar bunƙasa tattalin arziƙinta ba tare da dogaro da Amurka ba.

“Akwai hanyoyi da dama da za mu iya faɗaɗa tattalin arziƙinmu da ƙarfafa haɗin kan soji ba tare da dogaro da su ba,” in ji Gumi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Maganin Nankarwa (3)
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m