Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda
Published: 31st, March 2025 GMT
Wani yaro dan shekara hudu da ya kira wayar salular ’yan sandan yankin Mount Pleasant a Karamar Hukumar Charleston Jihar South Carolina da ke Amurka ya ce, mahaifiyarsa ta shanye masa ‘ice cream’ dinsa kuma yana bukatar a hukunta ta, a kai ta gidan yari saboda aikata hakan.
A cewar ’yan sanda yaron dan shekara 4 ya yi kururuwa, inda ya kira ’yan sanda bayan mahaifiyarsa ta shanye masa ice cream dinsa.
Al’amarin ya faru ne a cikin a garin Mount Pleasant, Wisconsin — mai nisan kilomita bakwai, yamma da Racine — lokacin da yaro dan shekara 4 ya tuntubi ‘yan sanda, inda ya ce, mahaifiyarsa ba ta kyauta masa ba, a cewar wata sanarwa da ’yan sandan kauyen Mount Pleasant suka fitar.
“An aika jami’an ’yan sanda, wato Gardinier da Ostergaard don amsa kiran mai korafin neman agajin jami’an 911, wanda ya bayyana cewa, mahaifiyarsa ba ta kyauta masa kuma yana bukatar a kai ta gidan yari”, in ji hukumomi.
Lokacin da jami’ai suka isa gidansu, yaron ya ce, mahaifiyarsa ta shanye masa ‘ice cream’ dinsa kuma yana bukatar a ka ita gidan yari saboda aikata hakan.
Daga bisani ya kuma shaida wa ’yan sanda cewa, ba ya son a kai mahaifiyarsa gidan yari kawai, yana son a biya shi ‘icecream’ da ta shanye masa.
Daga baya jami’an sun bar gidan bayan sun gano cewa, wannan shi ne dalilin da ya sa aka kira su, amma sun dawo washegari, wanda a wannan karon suka ba wa yaron mamaki, inda suka kawo masa ice cream, “bayan ya yanke shawarar cewa ba ya son mahaifiyarsa ta shiga matsala,” in ji ’yan sanda.
Jami’an ’yan sandan da suka amsa kiran, ba su kaɗai ne suka gano abin dariya game da lamarin ba.
“Ban ce yana da gaskiya ba. Abin da nake fada shi ne na fahimta,” in ji wani mutum da ke mayar da martani ga ofishin ’yan sanda na kauyen Mount Pleasant game da lamarin a shafukan sada zumunta na zamani.
“Aƙalla ya san yadda ake kiran lambar taimako ko neman agajin jami’an tsaro,” in ji wata. “Zai iya ceton ran wani wata rana!”
Jami’an ’yan sandan da suka ziyarci gidan su yaron sun dauki hoto tare da yaron mai shekara 4 bayan an warware matsalar, inda suka samu damar yin barkwanci.
“Ina son jin labarin jami’anmu game da abin ban mamaki, inda suke samar da kyakkyawar dangantaka tsakaninsu da yara,” in ji wani mai amfani da kafofin sada zumunta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yaro mahaifiyarsa ta
এছাড়াও পড়ুন:
Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
A yau Litinin ne dai kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa su ka yi taron gaggawa a birin Doha na kasar Qatar da aka tattauna harin wuce gona da iri da HKI ta kai wa kasar.
Bayanin bayan taron ya kunshi bangarori mabanbanta da su ka hada da daukar matakai kwarara domin taka wa HKI birki akan ta’addancin da take yi, da kuma hanyoyin kare kai anan gaba.
Kungiyar kasashen larabawan yankin tekun fasha ta sake jaddada muhimmancin aiki da dokar kafa rundunar hadin gwiwa ta kare kai daga duk wani wuce gona da iri daga waje.
Bugu da kari, mahalarta taron sun amince da dukar dukkanin matakan dokoki a fagen duniya domin hukunta jami’an HKI da su ka tafka laifukan yaki.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci