HausaTv:
2025-07-31@11:15:56 GMT

Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba

Published: 30th, March 2025 GMT

Shugaban majalisar mulkin kasar Sudan kuma kwamandan Sojin kasar Abdel Fattah al-Burhan ya tabbatar da cewa, farin cikin samun nasara a Sudan ba zai cika ba har sai an kawar da tungar karshe ta mayakan RSF a kasar, yana mai jaddada cewa kasar ba za ta ja da baya ba har sai an murkushe wadannan mayakan ‘yan tawaye, wadanda suka aikata munanan laifuka kan al’ummar Sudan.

Al-Burhan ya yi nuni da cewa, za a ci gaba da gwabzawa har sai an samu cikakken adalci, yayin da ya tabbatar da cewa ya tsaya tsayin daka da dukkan ‘yan kasar, kuma ya yi imani da ci gaba da kokarin maido da tsaro da kwanciyar hankali a kowane sako  na kasar Sudan.

Al-Burhan ya ce: Har yanzu hanyar zaman lafiya da kawo karshen yakin a bude take, kuma duk wannan abu ne mai yiyuwa, kuma hanya a fili take, wato kungiyar RSF ta ajiye makamanta.

Ya tabbatar da cewa babu wata niyya ta tattaunawa da Rundunar ta RSF a yanzu, inda ya bayyana cewa kofar yin afuwa a bude take ga duk wanda ya ajiye makamansa. A ranar Asabar din da ta gabata ce sojojin kasar Sudan suka sake karbe ikon Kasuwar Libiya da ke yammacin birnin Omdurman, lamarin da ke nuna wani gagarumin mataki na ci gaba da suke samu, wanda ya biyo bayan sake kwac fadar shugaban kasa daga hannun dakarun RSF da sojojin na Sudan suka yi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya bayyana cewa Iran a shirye take ta fadada hulda da kasashen turai, amma kuma wannan ba zai sa ta saryar da hakkinta na sarrafa makamashin nukliya karshen dokokin kasa da kasa wadanda suka amince mata ta yi haka ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a yau Litinin a lokacinda yake ganaw da sabon jakadan kasar Faransa a Tehran pierre Cochard wanda ya mika masa tarkardun fara aikinbsa.

Shugaban ya kara da cewa an takurawa kasar Iran dangane da shirinta na makamashin nukliya a bayan. Amma daga yanzun kuma ba zata amince da irin takurawa ta bay aba.

Ya kuma bayyana cewa tattaunawa tsakanin Iran da kasashe uku na turai wato Faransa da Jamus da kuma Burtaniya, saboda samun fahintar juna da kuma daukewa kasar takunkuman tattalin arzikinn da turawan suka dora mata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Man Utd Na Tattaunawa Da Golan PSG, Chelsea Ta Nace Wa Garnacho
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa